• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Taska Tsarin da Muka Fitar Don Tallafawa Yaran da Basa Zuwa Makaranta –...
  • Taska

Tsarin da Muka Fitar Don Tallafawa Yaran da Basa Zuwa Makaranta – Dr. Umar Buba Bindir

By
Web Engineer
-
February 20, 2022
Arewa Award

Tsarin da Muka Fitar Don Tallafawa Yaran da Basa Zuwa Makaranta – Dr. Umar Buba Bindir

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya nuna cewa Najeriya ta shige gaba, wajen yawan yaran da ba su zuwa makaranta a faɗin Najeriya, da adadin yara miliyan 13 da ke zaune a gida, ko suke gararamba a gari.

Bayan waɗannan alƙaluma na MDD tuni gwamnatin Najeriyar ta ce ta fara wani bincike domin kididdige yawan yaran da ba su zuwa makaranta.

A cewar Shugaban shirin tallafa wa masu karamin karfi na kasar, wato National Social Investment Programme da ma’aikatar ayyukan jin kai ke gundanarwa, kawo yanzu an gudanar da aikin kidayar yaran a wasu jihohi.

Dr. Umar Buba Bindir, ya shaida wa BBC cewa, shugaba Muhammadu Buhari ya kadu sosai a lokacin da ya ji alkaluman da aka fitar na yaran da su zuwa makaranta ya.

”Wannan dalili ne ya sa aka zauna aka yi nazari sosai saboda muhimmancin da ilimi ke da shi a cikin al’umma” in ji Dr bindir.

Read Also:

  • Gwamnan Kano ya aikewa Majalisar dokoki sunan wanda zai shugabanci hukumar yaki da cin hanci da rashawa
  • Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya
  • Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri

Ya ce,” Ba tare da bata lokaci ba shugaba Buhari ya bayar da umurnin a dauki matakin da ya dace wajen magance wannan matsala, inda ya ce me zai hana a gina makarantu a kusa da inda yaran suke, ta yadda ba za su rinka shan wahala wajen neman ilimin ba”

Ya ƙara da cewa ”Akwai hukumar kididdiga ta kasa tana nan tana bin garuruwa da kauyuka domin tantance yaran da ba su zuwa makaranta – in ji shugaban National Social Investment Programme.

Dr. Umar Buba Bindir, ya ce wannan matsala ta rashin zuwan yara makaranta ba arewacin Najeriya kadai ta shafa ba, ba in da babu inda ba ta shafa ba, saboda binciken da suke yi ya nuna hakan.

Ya ce, “A yanzu mun shirya nan da wata daya zuwa wata biyu cewa in sha Allah za a fara koya wa irin wadannan yara abubuwa hudu, wato turanci da lissafi da yadda za a zauna lafiya da kuma sana’a”.

”Sannan za mu rinka ciyar da su abinci sau uku (a rana), kuma an samar da malamai wadanda za su yi ta koya musu abubuwa tun safe har zuwa dare a kowacce rana”, in ji shi.

Ya ce, iyalan yaran kuma idan an gano su za a sanya su kan tsarin nan na basu naira dubu biyar a kowanne wata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • Dr.Umar Buba Kindir
  • Majalisar Dinkin Duniya
  • Makaranta
  • najeriya
  • National Social Investment Programme
  • Shugaba Buhari
Previous articleSojojin Najeriya Sun Hallaka Kwamandojin ISWAP a Sambisa
Next articleBisa Kuskure: Sojojin Najeriya Sun Kashe Yara 7 Tare da Jikkata 5
Web Engineer

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Azumin Bara: Talge Muka Riƙa Sha a Hannun Maharan Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna

Zambar N2.2bn: EFCC ta Sake Gurfanar da ɗan Tsohon Shugaban PDP

Magance Karancin Naira: CBN ya Umarci Bankuna da su yi Aiki a Ranakun Asabar da Lahadi

Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

Hukumar NITDA ta Gabatar da Satifiket ga Matan da Suka Samu Horo Kan Fasahar Zamani

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

An Gudanar Da Bikin Arewa Stars 30 Under 30 2022, Cikin Nasara

Manomi Yayiwa Wata Mata Yankan Rago

‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

Gidauniyar Malam Inuwa Da Kokarinta Na Ilmantar Da Mutanen Karkara Da Rugage

Gidauniyar Malam Inuwa ta Ɗauki Nauyin Koyar da Ƴa’yan Fulani Al-ƙur’ani

Bincike: Shin Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) ta ƙirƙiro da Tambayoyi Domin Tantance kungiyoyin Musulmi da Kirista a kidayar 2023? 

Recent Posts

  • Gwamnan Kano ya aikewa Majalisar dokoki sunan wanda zai shugabanci hukumar yaki da cin hanci da rashawa
  • Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya
  • Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri
  • KACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami’anta
  • Dino Melaye ya koma jam’iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDP

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1506 days 18 hours 46 minutes 57 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1488 days 20 hours 28 minutes 22 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Gwamnan Kano ya aikewa Majalisar dokoki sunan wanda zai shugabanci hukumar yaki da cin hanci da rashawaTinubu ya yi karin wa'adin Aiki ga shugaban Custom na NijeriyaGini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar MaiduguriKACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami'antaDino Melaye ya koma jam'iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDPMamakon ruwan sama ya haifar da ambaliya a MaiduguriAn samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴan bindiga - RibaduHadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar JigawaZanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke Kenyazamu hallaka Da;iban da ke hannun mu matukar baku biya Fansa ba - 'Yan BindigaGwamnan Zamfara ya Amince da Nadin Sabon Sarki GusauAkalla jami'an tsaron jihar Katsina 100 suka mutu a bakin aiki - KwamishinaYadda yan bindiga suka yiwa mutane 38 yankan RagoAmbaliyar ruwa ta lalata gidaje tare da kashe mutane 23 da a birnin YolaFadar shugaban Kasa ta magantu kan zargin da Kwankwaso ya yiwa Tinubu
X whatsapp