Home SIYASA Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta Saka Baki Cikin Rikicin Kasar Rasha da Ukraine

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta Saka Baki Cikin Rikicin Kasar Rasha da Ukraine

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta Saka Baki Cikin Rikicin Kasar Rasha da Ukraine

 

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta saka baki cikin rikicin da ke faruwa tsakanin kasar Rasha da Ukraine tana mai kira ga Rasha ta mayar da dakarunta gida.

Najeriya ta yi wannan kiran ne a wani taro da ta yi da wakilan kasashen G7 a ranar Juma’a a Abuja inda ta yi kira da bangarorin biyu su rungumi diflomasiyya da zaman lafiya.

Jakadan Jamus kuma shugaban G7, Birgitt Ory, ya yi wa Najeriya godiya bisa tofa saka baki a lamarin tana mai cewa muryar Najeriya na da muhimmanci a duniya kuma ya dace a ji matsayarta

Abuja- Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta gana da wakilan kasashen G7 a Najeriya inda ta nuna damuwar ta game da rikicin Rasha da Ukraine tana mai kira da a warware lamarin cikin zaman lafiya, rahoto Daily Trust.

Ministan harkokin kasashen waje, Goeffrey Onyeama, ya gana da wakilan a ranar Juma’a a Abuja, yana mai cewa gwamatin Najeriya ta yi kira da a zauna lafiya kuma a yi amfani da diflomasiyya da wurin warware matsalar cikin lumana.

Onyeama ya ce Najeriya bata goyon bayan matakin da Rasha ta dauka na amfani da karfin soji, tana mai kira ga Rasha ta janye dakarunta, rahoton The Punch.

“Dukkan bangarorin biyu su mayar da hankali wurin zaman lafiya da diflomasiyya.

“Muna goyon bayan duk wani mataki na dakatar da harin soji kuma dakarun Rasha su janye su koma Rasha,” a cewar Onyeama.

Jakadan Jamus ya yaba da matsayar Najeriya kan rikicin na Rasha da Ukraine

Da ya ke magana da manema labarai bayan taron na sirri, Jakadan Jamus a Najeriya, Birgitt Ory, wanda kuma shine shugaban G7 ya yaba da matakin Kungiyar Hadin kan Afirka, AU, kan rikicin.

Ory, wanda kuma ya jinjinawa Najeriya kan tofa albarkacin bakinta, ya ce Najeriya muhimmiyar murya ce da ya dace duniya ta ji daga gare ta.

Ya ce abin da ke a fili shine tir da hare-haren da dukkanin kasashen Majalisar Dinkin Duniya suka yi sakamakon harin da Rasha ta kai.

Ory ya ce matakan da Majalisar Dinkin Duniya da Kwamitin Kare Hakokin Bil Adama, wacce Najeriya mamba ce da wasunsu suka dauka yana da muhimmanci.

Sauran wadanda suka hallarci taron sun hada da jakadun Amurka, Birtaniya, EU, ECOWAS, Japan da Canada.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp