Home SIYASA Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta Saka Baki Cikin Rikicin Kasar Rasha da Ukraine

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta Saka Baki Cikin Rikicin Kasar Rasha da Ukraine

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta Saka Baki Cikin Rikicin Kasar Rasha da Ukraine

 

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta saka baki cikin rikicin da ke faruwa tsakanin kasar Rasha da Ukraine tana mai kira ga Rasha ta mayar da dakarunta gida.

Najeriya ta yi wannan kiran ne a wani taro da ta yi da wakilan kasashen G7 a ranar Juma’a a Abuja inda ta yi kira da bangarorin biyu su rungumi diflomasiyya da zaman lafiya.

Jakadan Jamus kuma shugaban G7, Birgitt Ory, ya yi wa Najeriya godiya bisa tofa saka baki a lamarin tana mai cewa muryar Najeriya na da muhimmanci a duniya kuma ya dace a ji matsayarta

Abuja- Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta gana da wakilan kasashen G7 a Najeriya inda ta nuna damuwar ta game da rikicin Rasha da Ukraine tana mai kira da a warware lamarin cikin zaman lafiya, rahoto Daily Trust.

Ministan harkokin kasashen waje, Goeffrey Onyeama, ya gana da wakilan a ranar Juma’a a Abuja, yana mai cewa gwamatin Najeriya ta yi kira da a zauna lafiya kuma a yi amfani da diflomasiyya da wurin warware matsalar cikin lumana.

Onyeama ya ce Najeriya bata goyon bayan matakin da Rasha ta dauka na amfani da karfin soji, tana mai kira ga Rasha ta janye dakarunta, rahoton The Punch.

“Dukkan bangarorin biyu su mayar da hankali wurin zaman lafiya da diflomasiyya.

“Muna goyon bayan duk wani mataki na dakatar da harin soji kuma dakarun Rasha su janye su koma Rasha,” a cewar Onyeama.

Jakadan Jamus ya yaba da matsayar Najeriya kan rikicin na Rasha da Ukraine

Da ya ke magana da manema labarai bayan taron na sirri, Jakadan Jamus a Najeriya, Birgitt Ory, wanda kuma shine shugaban G7 ya yaba da matakin Kungiyar Hadin kan Afirka, AU, kan rikicin.

Ory, wanda kuma ya jinjinawa Najeriya kan tofa albarkacin bakinta, ya ce Najeriya muhimmiyar murya ce da ya dace duniya ta ji daga gare ta.

Ya ce abin da ke a fili shine tir da hare-haren da dukkanin kasashen Majalisar Dinkin Duniya suka yi sakamakon harin da Rasha ta kai.

Ory ya ce matakan da Majalisar Dinkin Duniya da Kwamitin Kare Hakokin Bil Adama, wacce Najeriya mamba ce da wasunsu suka dauka yana da muhimmanci.

Sauran wadanda suka hallarci taron sun hada da jakadun Amurka, Birtaniya, EU, ECOWAS, Japan da Canada.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp