Home SIYASA Na Amince na Sasanta da Rasha a Iyakar Ukraine da Belarus –...

Na Amince na Sasanta da Rasha a Iyakar Ukraine da Belarus – Shugaban Ukraine

Na Amince na Sasanta da Rasha a Iyakar Ukraine da Belarus – Shugaban Ukraine

Shugaban Ukraine Volodymyr Zelinsky ya ce ya amince ya sasanta da Rasha a wani wuri kan iyakar Ukraine da Belarus

Mista Zelensky ya ce a tattaunawar da ya yi da shugaban Belarus Alexander Lukashenko, Ukraine ta amince ta gana da Rasha ba tare da wani sharaɗi ba a kan iyakar Ukraine da Belarus a kusa da kogin Pripyat.

Shugaban Ukraine ya ce Mista Lukashenko ya ce ya ɗauki alhakin tabbatar da dakatar da shawagin dukkanin jiragen sama, masu saukar angulu da masu kakkabo makamai mai linzame lokacin ziyarar domin tattaunawar tsakanin ɓangarorin biyu.

Tun da farko Msita Zelensky ya yi watsi da tayin Rasha na hawa teburin tattaunawa da Belarus. Ya ce ya fi buƙatar a tattauna a wata ƙasa saɓanin Belarus.

Belarus babbar aminiyar Rasha ce a yaƙin da take da Ukrainer.

Rasha ta sanar a ranar Lahadi cewa ta tura wakilai Belarus domin tattaunawa da jami’an Ukraine.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp