Home Labarai ‘Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari...

‘Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari ta yi Hatsari a Jahar Delta

‘Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari ta yi Hatsari a Jahar Delta

Daya daga cikin motocin da ke cikin ayarin shugaban ma’aikatan Buhari, Ibrahim Gambari, da minista Fashola da takwaransa Ngige sun yi hatsari a Asaba, jihar Delta.

‘Yan sanda hudu ne ake fargabar sun mutu a hatsarin wanda aka ce ya faru ne da yammacin ranar Talata, 8 ga watan Maris.

Rahotanni sun ce manyan jami’an gwamnatin sun je babban birnin jihar Delta ne domin duba wata gada da aka gina.

Asaba, jihar Delta – Ayarin shugaban ma’aikata, Ibrahim Gambari; Ministan Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola; da takwaransa na ma’aikatar kwadago da samar da aikin yi, Christ Ngige, sun yi hatsari a yammacin ranar Talata, 8 ga watan Maris.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa hatsarin ya afku ne a yayin duba wata gada a garin Asaba na jihar Delta, inda rahoton ya kara da cewa ‘yan sanda hudu ne ake fargabar sun mutu.

An tattaro cewa direban motar ne ya rude yayin tuka motar da ke dauke da jami’an tsaro inda ta fada cikin wani rami mai zurfi.

Shaidun gani da ido sun bayyana yadda lamarin ya faru

Wani shaidan gani da ido, John Okorie, ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da motar da ke dauke da wadanda lamarin ya rutsa dasu ke tattaunawa kan kwanar da ta kai ga wajen aikin gina gadar Neja ta biyu a Asaba.

An tattaro cewa motar ‘yan sandan ta yi gudu ne don haduwa da sauran tawagar motocin ministocin ne a lokacin da ta kauce daga titi kuma ta yi hatsari.

Har ila yau, wani direba a Delta, wanda bai bayyana sunansa ba, ya ce:

“Lamarin ya yi muni matuka.

“Direba dan sandan yana gudu yayin da ake tattaunawa kan lankwasar hanyar wanda saboda gudun ya kasa sarrafa motar. Suka fada cikin wani rami mai zurfi. Ni ina bin bayan ayarin, ina tuki na a hankali.

“Da taimakon wasu mutane mun ceto hudu daga cikinsu amma sun samu munanan raunuka. Suna ta ihu yayin da motar ta fado musu.”

Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Delta, DSP Bright Edafe, ya ce har yanzu bai samu rahoton faruwar hatsarin ba.

Karin bayani nan tafe…

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp