Home SIYASA Ma’aikatar Bada Agaji ta Kafa Cibiyoyi Takwas Domin Kula da Wadanda su...

Ma’aikatar Bada Agaji ta Kafa Cibiyoyi Takwas Domin Kula da Wadanda su ke Sansanin Gudun Hijira a Garuruwan Zamfara – Kwamishinan Jahar

Ma’aikatar Bada Agaji ta Kafa Cibiyoyi Takwas Domin Kula da Wadanda su ke Sansanin Gudun Hijira a Garuruwan Zamfara – Kwamishinan Jahar

 

Gwamatin Zamfara ta na dawainiya da mutane fiye da 700, 000 da matsalar rashin tsaro ta shafe su.

Ibrahim Magaji Dosara wanda shi ne Kwamishinan yada labaran Zamfara ne ya bayyana wannan.

Kwamishinan tsaro ya ce gwamnatin Muhammad Bello Matawalle ta dauki ‘yan banga har 4200 aiki.

Kaduna – gwamnatin jihar Zamfara ta ce ma’aikatar bada agaji ta kafa cibiyoyi takwas domin kula da wadanda su ke sansanin gudun hijira a garuruwan jihar.

Daily Trust ta rahoto gwamnatin ta na cewa akwai sama da mutane 700, 000 da ke gudun hijira.

Kwamishinan yada labarai na Zamfara, Ibrahim Magaji Dosara ya shaidawa manema labarai a Kaduna cewa gwamnati na dawainiya da masu gudun hijira.

Alhaji Ibrahim Magaji Dosara ya ce a kowace karamar hukuma da ke jihar Zamfara, akwai jami’an bada agaji na gaggawa da aka samar domin su bada taimako.

Wadannan jami’ai za su rika bada tallafi ga wadanda matsalar tsaro ta shafa a kowace karamar hukuma.Akwai kananan hukumomi 14 ne a jihar ta Zamfara.

“Baya ga rabon kayan abinci, katifa, gado, tufafi da sauransu da gwamnatin jiha ta ke yi, ma’aikatar ta na yabon kokarin da kungiyoyin kasashen waje ke yi.”

“Wadannan kungiyoyi su na karfafawa gwamnatin jihar ta hanyar bada kudi ga masu gudun hijira, ana raba N30000 zuwa N40000 ga wadanda abin ya shafa.”

“Gwamnatin tarayya ta narka makudan kudi a kan haka Gwamnatin Zamfara ta na godewa duk wadanda suka taimaka wajen yaye wa mutanenta bakin ciki.” – Alhaji Ibrahim Magaji Dosara

An rahoto kwamishinan yana cewa ana horas da wadanda ‘yan bindiga suka fatattaka.Ana koya masu tukin keke napep, tela, hada ruwa, wanzaci da sauransu.

An dauki ‘yan sa-kai Kwamishinan tsaro da harkokin gida, Mamman Ibrahim Tsafe ya ce sun dauki ma’aikatan sa-kai 4200 aikin banga domin su kare jama’a daga ta’adin ‘yan bindiga.

DIG Mamman Tsafe ya ce an koyawa ma’aikatan rike makami domin su taimakawa jamii’an tsaro.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp