Home SIYASA APC Zuwa PDP: Masoyin ɗan Siyasa ya Salwanta Rayuwarsa Gurin Murnar Sauya...

APC Zuwa PDP: Masoyin ɗan Siyasa ya Salwanta Rayuwarsa Gurin Murnar Sauya Shekar Uban Gidansa a Abuja

APC Zuwa PDP: Masoyin ɗan Siyasa ya Salwanta Rayuwarsa Gurin Murnar Sauya Shekar Uban Gidansa a Abuja

Wani masoyi ɗan gani kasheni na shugaban karamar hukuma a Abuja ya rasa rayuwarsa sanadiyyar hatsarin mota.

Mutumin ya rasu ne yayin da suke tsaka murnar sauya shekar Uban Gidansa Ciyaman na Gwagwalada daga APC zuwa PDP.

Sauran mutum uku da suke cikin motar suna kwance a Asibiti, Mamacin kuma an masa jana’iza yadda musulunci ya koyar.

Abuja – Wani magoyin baya kuma ɗan a mutun shugababan ƙaramar hukumar Gwagwalada a a babban birnin tarayya Abuja, ya rasa rayuwarsa a hatsarin Mota.

Daily Trust ta rahoto cewa mutumin mai suna Awwal Idris, ya rasu ne yana tsaka da murnanr sauya shekar Uban gidansa Ciyaman, Alhaji Adamu Mustapha, daga APC zuwa PDP.

Rahoto ya tabbatar da cewa ragowar mutum uku dake tare da Mamacin a cikin Motar, yanzu haka suna kwance a wani Asibitin kuɗi dake Gwagwalada, Abuja.

Lamarin ya auku ranar Asabar da misalin ƙarfe 11:00 lokacin da tawagar Ciyaman din ke kan hanyar zuwa gundumar Dobi, inda zai tabbatar da sauya sheƙarsa a hukumance ta hannun shugaban PDP na Dobi, Abubakar Sarki.

Yadda mutumin ya rasa rayuwarsa a hatsarin

Bayanan da muka samu sun nuna mana cewa Motar da suke ciki ta sauka daga kan titi kuma ta wuntsila sannan ta dira a cikin hanyar ruwa dake bakin titin.

Bisa haka ne, Idris ya rasa rayuwar nan take a inda hatsarin ya auku, sauran kuma aka garzaya da su Asibitin domin kula da lafiyarsu.

Shugaban jam’iyyar PDP na karamar hukumar Gwagwalada, Alhaji Yunusa Abdullahi, ya tabbatar da faruwar hatsarin ga manema labarai ta wayar Salula.

Ya ce Mamacin, wanda ya fito daga ƙaramar hukumar Leda, inda Ciyaman na Gwagwalada ya fito, an masa jana’iza kamar yadda Addinin Musulunci ya tanadar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp