Home SIYASA Bayan Tsige ‘Yan Majalisa 20: ‘Yan Sanda Sun Mamaye Harabar Majalisar Dokokin...

Bayan Tsige ‘Yan Majalisa 20: ‘Yan Sanda Sun Mamaye Harabar Majalisar Dokokin Jahar Cross River

Bayan Tsige ‘Yan Majalisa 20: ‘Yan Sanda Sun Mamaye Harabar Majalisar Dokokin Jahar Cross River

An tsaurara matakan tsaro a harabar majalisar dokokin jihar Cross River.

Hakan ya biyo bayan tsige yan majalisa 20 da babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi a ranar Litinin kan sauya sheka daga PDP zuwa APC.

Jami’an yan sanda na sashi daban-daban ne suka karbe majalisar tun daga karfe 6:00 na asuba.

Cross River – Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa sashi daban-daban na rundunar yan sandan Najeriya sun karbe dukka hanyoyin da ke sada mutum ga harabar majalisar dokokin jihar Cross River.

Sun mamaye wuraren ne tun da misalin karfe 6:00 na asubahi kamar yadda shaidu suka bayyana.

Sashin yan sandan da ke kasa sun hada da na yaki da garkuwa da mutane, masu yaki da kungiyar asiri da kuma jami’an yan sanda na yau da kullum, dukkansu dauke da makamai.

The Sun ta kuma rahoto cewa an hangi wasun su na cikin harabar majalisar dokokin.

An kuma gano wasu daga cikin jami’an yan sandan tsaye kusa da ofishin Gwamna Ben Ayade wanda bai da nisa da wajen.

A daya bangaren majalisar akwai filin wasa na UJ Esuene Stadium Calabar. An kuma gano wasu mutane da ake zaton magoya bayan jam’iyyar siyasa ne suna zukar hayaki da shan lemuka masu zafi.

Masu ababen hawa da masu wucewa na fuskantar matsala wajen kutsawa cikin cunkoson jami’an tsaro da motocinsu.

An tattaro cewa an tsaurara matakan tsaron ne biyo bayan hukuncin da mai shari’a Taiwo Taiwo ya yanke a wata babbar kotun tarayya da ke Abuja inda ta kori ‘yan majalisar jihar 18 da kuma wasu ‘yan majalisar wakilai guda biyu kan sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar All Progressives Congress.

Jam’iyyar APC mai mulki ta yi ikirarin cewa ta shigar da kara kotu domin a dakatar da aiwatar da hukuncin, yayin da jam’iyyar ta garzaya zuwa kotun daukaka kara.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp