Home SIYASA Rikicin Rasha da Ukraine: Kada Wanda ya ci ko Sha Wani Abu...

Rikicin Rasha da Ukraine: Kada Wanda ya ci ko Sha Wani Abu a Wajen Taron Neman Zaman Lafiya – Ministan Ukraine

Rikicin Rasha da Ukraine: Kada Wanda ya ci ko Sha Wani Abu a Wajen Taron Neman Zaman Lafiya – Ministan Ukraine

 

Ministan harkokin wajen Ukraine, Dmytro Kuleba, ya bai wa mahalarta taron tattaunawar da ake yi da Rasha shawara cewa kada wanda ya ci ko ya sha wani abu a wajen.

Ministan ya ba da shawarar ce gabanin fara taron da za a yi a Turkiyya.

Kafar yada labaran Ukraine ce ta bayyana hakan inda ta ce ministan ya bada shawararce bayan zargin da aka yi cewa an bai wa shahararren attajirin nan Roman Abramovich guba a farkon tattaunawar zaman lafiyar da aka yi a farkon watan nan.

Akwai shakku a kan zargin da ake a kan zargin bai wa Mr Abramovich guba, inda wani jami’a a Amurka da ba a bayyana sunansa ba ya shaida wa kamfanin dillancin na Reuters cewa ba mamaki canjin yanayi ne ya shafi Mr Abramovich.

A ci gaba da tattaunawar ta yau a kan rikicin Rasha da Ukraine, Abramovich ya isa wajen a cewar kafar yadda labaran Turkiyya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp