Home SIYASA An Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo

An Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo

Jagoran jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, kuma Dan Takarar Shugabancin Qasa karkashin Inuwar Jam’iyyar, Bola Ahmad Tinubu yace Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osibanjo ba Dan sa bane.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai a yammacin ranar Litinin a Birnin Tarayya Abuja, jim kadan bayan kammala ganawar sa da Gwamnonin Jam’iyyar APC su 12.

Ganawar da aka yi a masaukin Gwamnan Jihar Kebbi, a Asokoro dake Birnin tarayya Abuja, ta zo bayan Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osibanjo ya bayyana Kudirin sa na tsayawa takarar Shugaban Kasa a kakar zaben shekarar 2023.

Da aka tambaye shi don yin tsokaci dangane da Takarar Mataimakin Shugaban Kasar, wanda ake masa kallon dansa ne a siyasance, Tinubu yace “Bani da wani da da ya girma da zai iya yin Takarar shugaban kasa, “Bani da wani Da daya girma zai iya wannan furuci.

Sai dai yace ya ganawa da gwamnonin jihohin ne domin neman hadin kai, goyon baya da karfafa Gwuiwa dangane da burin sa na tsayawa takarar shugabancin Nijeriya a shekarar 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp