Home Labarai CIN HANCI: EFCC Ta Kwace Jami’a, Masana’anta, Otal Mallakin Daraktan Kudi

CIN HANCI: EFCC Ta Kwace Jami’a, Masana’anta, Otal Mallakin Daraktan Kudi

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati a Nijeriya  ta EFCC ta kwace Jami’a, Masana’anta, Otal dake da alaka da daraktan kudi.

Wannan na kunshe ta cikin wata takardar sanarwa da aka raba ga manema labarai mai dauke da sa hannun kakakin hukumar ta EFCC Wilson Uwajaren, mai kwanan watan 1 ga watan Yunin 2022.

Babbar kotun tarayya dake zaman ta a Birnin tarayyar kasar Abuja, a yayin zaman shari’ar daya gudana ranar laraba 1 ga watan Yuni 2022, ta bada Umarnin karbe dukkan wata kadara dake da alaka da jami’ar NOK,  wadda ke jihar Kaduna.

Jami’ar wadda tsohon daraktan Kudi na DFA a ma’aikatar lafiya ta tarayya Anthony Hassan ya gina, ana zargin an gina ta ne daga kudaden haramun da aka bi diddigin mamallakin jami’ar.

Hassan ya rike mukabin Daraktan Kudin na DFA a ma’aikatar a tsakanin shekarar 2016 zuwa 2019, ana zargin ya gina jami’ar ne da kudin haramun, yanzu dai haka akwai gine-ginen da suka hadar ginin majalisar zartarwar jami’ar, ginin shahen ICT, Sashen Nazari da kirkirar Magunguna, sashen kimiyya, gine-gine shashen manyan Malamai Ajujuwan karatu da suran gine-gine.

Sauraran kadarorin da aka gani mallakin Hassan, wadanda kuma aka kwace su na wucin gadi sun hadar da Gwasmyen water factory, Gwasmyen Event Center da Gwasmyen International Hotel dake jihar kaduna.

Mai shari’a Zainab Abubakar, ta bayar da umarnin kwace kadarorin na wucin gadi yayin da take yanke hukunci kan karar da hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ta EFCC ta shigar gabanta.

Lauyan hukumar ta EFCC Ekele Iheanacho ya shaidawa kotun cewa hukumar na neman wannan umarni ne dogaro da sashi na 44 (2) na kudin tsarin mulkin nijeriya na shekara 1999 (wanda aka yiwa gyaran fuska) da kuma sashe na 17 na kudin yaki da Zamba, laifukan da suka dangaci doka mail amba ta 14, 2006 da kuma karkashin ikon kotun mai girma.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp