Home Labarai Babban Mai Tace Labarai Na Jaridar PRNigeria Ya Rasa Mahaifin Sa.

Babban Mai Tace Labarai Na Jaridar PRNigeria Ya Rasa Mahaifin Sa.

Babban mai tace labarai na jaridar PRNigeria, Yusha’u Shuib ya rasa mahaifin sa Shiek Abdulhameed Agaka mai kimanin shekaru 77 a duniya.

Sheik Abdulhameed, sananne addinin islama ne kuma babban limamin garin Agaka dake karamar hukumar Ilorin da yamma dake jihar kwara, ya koma ga mahaccinsa sakamakon wata gajiriyar rashin lafiya a ranar asabar.

Tunu aka gudanar da jana’idar sa kamar yadda addinin musulunci ya tanadar a ranar lahadi a gidan sa dake garin na Agaka.

An haifi malamin a zuri’ar Imam Shuaib Said, mashahurin malamin addini, kuma masanin Al’kurani mai tsarki jagoran addinin muslunci a garin na Agaka.

Babban limamn na Agaka yayi karatun sa a makarantar School for Arabic Studies wato (SAS) dake jihar Kano daga bisani ya tafi Jami’ar Bayero dake jihar ta kano inda ya sami babban Digiri a fannin ilimin Alqur’ani a da kuma Nahawun Harshen Larabci.

Shaihin malamin a lokuta da daban-daban ya kasance shugaban sashen Nazarin harshen larabci a kwalejin ilimin addinin Musulunci da shari’a ta kano wato Aminu kano College of legal and Islamic studies.

Fatan Allah ya gafarta masa ya kuma inganata abinda ya bari yasa Aljanna ce makomar sa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp