Home Labarai Babban Mai Tace Labarai Na Jaridar PRNigeria Ya Rasa Mahaifin Sa.

Babban Mai Tace Labarai Na Jaridar PRNigeria Ya Rasa Mahaifin Sa.

Babban mai tace labarai na jaridar PRNigeria, Yusha’u Shuib ya rasa mahaifin sa Shiek Abdulhameed Agaka mai kimanin shekaru 77 a duniya.

Sheik Abdulhameed, sananne addinin islama ne kuma babban limamin garin Agaka dake karamar hukumar Ilorin da yamma dake jihar kwara, ya koma ga mahaccinsa sakamakon wata gajiriyar rashin lafiya a ranar asabar.

Tunu aka gudanar da jana’idar sa kamar yadda addinin musulunci ya tanadar a ranar lahadi a gidan sa dake garin na Agaka.

An haifi malamin a zuri’ar Imam Shuaib Said, mashahurin malamin addini, kuma masanin Al’kurani mai tsarki jagoran addinin muslunci a garin na Agaka.

Babban limamn na Agaka yayi karatun sa a makarantar School for Arabic Studies wato (SAS) dake jihar Kano daga bisani ya tafi Jami’ar Bayero dake jihar ta kano inda ya sami babban Digiri a fannin ilimin Alqur’ani a da kuma Nahawun Harshen Larabci.

Shaihin malamin a lokuta da daban-daban ya kasance shugaban sashen Nazarin harshen larabci a kwalejin ilimin addinin Musulunci da shari’a ta kano wato Aminu kano College of legal and Islamic studies.

Fatan Allah ya gafarta masa ya kuma inganata abinda ya bari yasa Aljanna ce makomar sa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp