Home Labarai A karkashin Mulkin Buhari, An Hallaka Sama Da Mutum 3,478, An Sace...

A karkashin Mulkin Buhari, An Hallaka Sama Da Mutum 3,478, An Sace 2,256

Wani rahoton bincike a Najeriya ya ce akalla mutane dubu 3 da 478 aka kashe a Najeriya tsakanin watan Disambar bara zuwa Yunin bana, yayin da aka sace wasu dubu 2 da 256 sakamakon tabarbarewar tsaron da ya addabi kasar.

Kungiyar da ke sanya ido akan harkokin tsaro da ake kira ’Nigeria Security Tracker’ da ke samun goyan bayan wata Majalisa a Amurka ta gabatar da wadannan alkaluma masu tada hankali.

Rahotan kungiyar ya danganta kisan da kuma sace mutanen da akayi a cikin watanni 7 da suka gabata da ayyukan ‘Yan ta’adda da ‘Yan bindiga da ‘Yan fashi da makami da ‘Yan kungiyar asiri da kuma jami’an tsaro.

Alkaluman da kungiyar ta gabatar yace a watan Disambar bara, an kashe ‘Yan Najeriya 342, yayin da aka sace wasu 397, cikin wadanda aka kashe harda manoma 45 a Jihar Nasarawa da kuma mata 34 da aka sace a Jihar Zamfara.

A watan Janairun wannan shekara, kungiyar tace akalla mutane 844 aka kashe, yayin da aka sace 603, cikin su harda mutane sama da 200 a yankunan Jihar Zamfara da 220 da aka kasha a Neja, sai kuma 200 da aka sace a Jihar.

A watan Fabarairu kuma, kungiyar tace mutane 495, bayan sace 326, cikin su harda 33 wadanda suka ki biyan harajin naira miliyan 40 da yan bindiga suka sanya musu a Jihar Zamfara, sai kuma 44 da aka kashe a Jihar Neja, tare da sace 31.

Sakamakon binciken yace a watan Maris, mutane 606 akayi asarar rayukan su, tare da sace wasu 450 cikin su harda Yan Sakai 63 a Jihar Kebbi da kuma mutane 26 da aka kashe a harin da ake danganta shi da ramako a Jihar Taraba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp