Home Labarai ‘Yan Jarida Mata Sun Wallafa Littafi A Wani Bangare Na Bikin Zagayowar...

‘Yan Jarida Mata Sun Wallafa Littafi A Wani Bangare Na Bikin Zagayowar Haihuwar Yahaya Bello

Mawallafan Gungun rukunin Kamfanin Image Merchants Promotion Limited (IMPR), PRNigeria, Economic Confidential, Politics Digest, sun kaddamar da wani littafi da wasu mata ‘yan jarida biyu suka rubuta akan Gwamnan jihar Koji Yahaya Bello a bikin cikar sa shekaru 47 da haihuwa.

Littafin mai suna “Yahaya Bello: 47 Narratives on a Change Agent,” an gabatar da  shi ga gwamnan yayin bikin cikar shekarar sa 47 da haihuwa a birnin tarayya Abuja.

Babbar wakiliya a jaridar Politics Digest Nafisat Bello da kuma wakiliyar jaridar tattalin arziki ta Economic Confidential Hafsat Ibrahim ne suka rubuta littafin mai shafuka 183, wanda ya kunshi siyakin gami da bayanin ayyukan Gwamna Yahaya Bello guda 47, wanda marubutana suka fara tattarawa tun a watan oktoban shekarar da ta gabata.

Da yake jawabi babban jami’in kamfanin na IMPR, Yusha’u A. Shuaib, yace wadannan siyakin ayyuka 47 da suka tattara yayi daidai da adadin shekarun da Gwamnan na haihuwa, inda ya kawo gagarumin cigaba a fannin tsaro, tattalin Arziki, gami da samar da ababen more rayuwa, ayyukan yi, karfafa mata da matasa da kuma yunkirinsa na neman kujera mafi girma a Nijeriya a ‘yan tsakanin nan.

Da yake bayyana jin dadin sa game da Littafin Yahaya Bello ya Godewa Alh. Shuiab bisa wannan kyautar bazata da aka yi masa a ranar zagayowar haihuwar sa tare da yin alkawarin cigaba da yin aiki tukuru don ganin an cigaba da samun cigaba mai dorewa a jihar ta Kogi.

Ya kuma nuna godiyar sa ga marubutan mata guda biyu, wadanda ‘yan asalin jihar Kogi ne, ya kuma yaba da jajircewarsu, sadaukar, tare da tabbatuwa akan wannan  gwadabe na aikin da suka dauke tun a shekarar data gabata.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp