Home Labarai ‘Yan Jarida Mata Sun Wallafa Littafi A Wani Bangare Na Bikin Zagayowar...

‘Yan Jarida Mata Sun Wallafa Littafi A Wani Bangare Na Bikin Zagayowar Haihuwar Yahaya Bello

Mawallafan Gungun rukunin Kamfanin Image Merchants Promotion Limited (IMPR), PRNigeria, Economic Confidential, Politics Digest, sun kaddamar da wani littafi da wasu mata ‘yan jarida biyu suka rubuta akan Gwamnan jihar Koji Yahaya Bello a bikin cikar sa shekaru 47 da haihuwa.

Littafin mai suna “Yahaya Bello: 47 Narratives on a Change Agent,” an gabatar da  shi ga gwamnan yayin bikin cikar shekarar sa 47 da haihuwa a birnin tarayya Abuja.

Babbar wakiliya a jaridar Politics Digest Nafisat Bello da kuma wakiliyar jaridar tattalin arziki ta Economic Confidential Hafsat Ibrahim ne suka rubuta littafin mai shafuka 183, wanda ya kunshi siyakin gami da bayanin ayyukan Gwamna Yahaya Bello guda 47, wanda marubutana suka fara tattarawa tun a watan oktoban shekarar da ta gabata.

Da yake jawabi babban jami’in kamfanin na IMPR, Yusha’u A. Shuaib, yace wadannan siyakin ayyuka 47 da suka tattara yayi daidai da adadin shekarun da Gwamnan na haihuwa, inda ya kawo gagarumin cigaba a fannin tsaro, tattalin Arziki, gami da samar da ababen more rayuwa, ayyukan yi, karfafa mata da matasa da kuma yunkirinsa na neman kujera mafi girma a Nijeriya a ‘yan tsakanin nan.

Da yake bayyana jin dadin sa game da Littafin Yahaya Bello ya Godewa Alh. Shuiab bisa wannan kyautar bazata da aka yi masa a ranar zagayowar haihuwar sa tare da yin alkawarin cigaba da yin aiki tukuru don ganin an cigaba da samun cigaba mai dorewa a jihar ta Kogi.

Ya kuma nuna godiyar sa ga marubutan mata guda biyu, wadanda ‘yan asalin jihar Kogi ne, ya kuma yaba da jajircewarsu, sadaukar, tare da tabbatuwa akan wannan  gwadabe na aikin da suka dauke tun a shekarar data gabata.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp