Home Labarai ‘Yan Jarida Mata Sun Wallafa Littafi A Wani Bangare Na Bikin Zagayowar...

‘Yan Jarida Mata Sun Wallafa Littafi A Wani Bangare Na Bikin Zagayowar Haihuwar Yahaya Bello

Mawallafan Gungun rukunin Kamfanin Image Merchants Promotion Limited (IMPR), PRNigeria, Economic Confidential, Politics Digest, sun kaddamar da wani littafi da wasu mata ‘yan jarida biyu suka rubuta akan Gwamnan jihar Koji Yahaya Bello a bikin cikar sa shekaru 47 da haihuwa.

Littafin mai suna “Yahaya Bello: 47 Narratives on a Change Agent,” an gabatar da  shi ga gwamnan yayin bikin cikar shekarar sa 47 da haihuwa a birnin tarayya Abuja.

Babbar wakiliya a jaridar Politics Digest Nafisat Bello da kuma wakiliyar jaridar tattalin arziki ta Economic Confidential Hafsat Ibrahim ne suka rubuta littafin mai shafuka 183, wanda ya kunshi siyakin gami da bayanin ayyukan Gwamna Yahaya Bello guda 47, wanda marubutana suka fara tattarawa tun a watan oktoban shekarar da ta gabata.

Da yake jawabi babban jami’in kamfanin na IMPR, Yusha’u A. Shuaib, yace wadannan siyakin ayyuka 47 da suka tattara yayi daidai da adadin shekarun da Gwamnan na haihuwa, inda ya kawo gagarumin cigaba a fannin tsaro, tattalin Arziki, gami da samar da ababen more rayuwa, ayyukan yi, karfafa mata da matasa da kuma yunkirinsa na neman kujera mafi girma a Nijeriya a ‘yan tsakanin nan.

Da yake bayyana jin dadin sa game da Littafin Yahaya Bello ya Godewa Alh. Shuiab bisa wannan kyautar bazata da aka yi masa a ranar zagayowar haihuwar sa tare da yin alkawarin cigaba da yin aiki tukuru don ganin an cigaba da samun cigaba mai dorewa a jihar ta Kogi.

Ya kuma nuna godiyar sa ga marubutan mata guda biyu, wadanda ‘yan asalin jihar Kogi ne, ya kuma yaba da jajircewarsu, sadaukar, tare da tabbatuwa akan wannan  gwadabe na aikin da suka dauke tun a shekarar data gabata.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp