Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Binne Ma’aikacin Poly Bayan Sun Karbi Miliyan 4

‘Yan Bindiga Sun Binne Ma’aikacin Poly Bayan Sun Karbi Miliyan 4

‘Yan bindiga sun hallaka ma’aikacin makarantar Polytechnic ta Talata-Mafara a jihar Zamfara Sanusi Halliru bayan sun karbi kudin fansar sa Naira miliyan 4.

‘Yan ta’addan sun yi garkuwa dashi ne akan hanyar Abuja zuwa Kaduna inda yake kokarin zuwa wajen wani taron karawa juna sani kafin yiwa kasa hidima.

Sun bukaci a biya naira miliyan 4 a matsayin kudin fansa, sai dai ba’a biya su kudin akan lokacin ba hakan ta sanya su halaka shi tare da binne gawar a cikin daji,

Wani makusanci mamacin, Muhammad Nasir, yace bayan sun tara miliyan Hudun sun kira ‘yan bindigar domin su fadi inda zasu kawo musu kudin su fanshi dan uwan su.

“Shugaban ‘yan bindigar ya fada mana lokaci da kuma wanda zai zo domin karbar kudin”. Amm da muka isa wajen bamu iske kowa ba.

“Sai daga bisani muka hangi wasu mutane saman Babura, da zuwan su suka bukaci mu basu kudin.

“Mun kuma mmika kudin gare su, said ai guda cikin su yace mana tuni dan uwan mu ya mutu.

“Mun bukaci su bamu gawar domin yi masa sutura kamar yadda Addini ya tanada, amma ga mamakin mu sai suka ce ai ya dade da mutuwa don haka sun binne shi.

“Sannan suka juya hankali kwance suka koma inda suka fito, Nasir ya bayyana hakan cikin bakin ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp