Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Binne Ma’aikacin Poly Bayan Sun Karbi Miliyan 4

‘Yan Bindiga Sun Binne Ma’aikacin Poly Bayan Sun Karbi Miliyan 4

‘Yan bindiga sun hallaka ma’aikacin makarantar Polytechnic ta Talata-Mafara a jihar Zamfara Sanusi Halliru bayan sun karbi kudin fansar sa Naira miliyan 4.

‘Yan ta’addan sun yi garkuwa dashi ne akan hanyar Abuja zuwa Kaduna inda yake kokarin zuwa wajen wani taron karawa juna sani kafin yiwa kasa hidima.

Sun bukaci a biya naira miliyan 4 a matsayin kudin fansa, sai dai ba’a biya su kudin akan lokacin ba hakan ta sanya su halaka shi tare da binne gawar a cikin daji,

Wani makusanci mamacin, Muhammad Nasir, yace bayan sun tara miliyan Hudun sun kira ‘yan bindigar domin su fadi inda zasu kawo musu kudin su fanshi dan uwan su.

“Shugaban ‘yan bindigar ya fada mana lokaci da kuma wanda zai zo domin karbar kudin”. Amm da muka isa wajen bamu iske kowa ba.

“Sai daga bisani muka hangi wasu mutane saman Babura, da zuwan su suka bukaci mu basu kudin.

“Mun kuma mmika kudin gare su, said ai guda cikin su yace mana tuni dan uwan mu ya mutu.

“Mun bukaci su bamu gawar domin yi masa sutura kamar yadda Addini ya tanada, amma ga mamakin mu sai suka ce ai ya dade da mutuwa don haka sun binne shi.

“Sannan suka juya hankali kwance suka koma inda suka fito, Nasir ya bayyana hakan cikin bakin ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp