Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Binne Ma’aikacin Poly Bayan Sun Karbi Miliyan 4

‘Yan Bindiga Sun Binne Ma’aikacin Poly Bayan Sun Karbi Miliyan 4

‘Yan bindiga sun hallaka ma’aikacin makarantar Polytechnic ta Talata-Mafara a jihar Zamfara Sanusi Halliru bayan sun karbi kudin fansar sa Naira miliyan 4.

‘Yan ta’addan sun yi garkuwa dashi ne akan hanyar Abuja zuwa Kaduna inda yake kokarin zuwa wajen wani taron karawa juna sani kafin yiwa kasa hidima.

Sun bukaci a biya naira miliyan 4 a matsayin kudin fansa, sai dai ba’a biya su kudin akan lokacin ba hakan ta sanya su halaka shi tare da binne gawar a cikin daji,

Wani makusanci mamacin, Muhammad Nasir, yace bayan sun tara miliyan Hudun sun kira ‘yan bindigar domin su fadi inda zasu kawo musu kudin su fanshi dan uwan su.

“Shugaban ‘yan bindigar ya fada mana lokaci da kuma wanda zai zo domin karbar kudin”. Amm da muka isa wajen bamu iske kowa ba.

“Sai daga bisani muka hangi wasu mutane saman Babura, da zuwan su suka bukaci mu basu kudin.

“Mun kuma mmika kudin gare su, said ai guda cikin su yace mana tuni dan uwan mu ya mutu.

“Mun bukaci su bamu gawar domin yi masa sutura kamar yadda Addini ya tanada, amma ga mamakin mu sai suka ce ai ya dade da mutuwa don haka sun binne shi.

“Sannan suka juya hankali kwance suka koma inda suka fito, Nasir ya bayyana hakan cikin bakin ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp