Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan ihar Zamfara Na Samun Nasara A Yakin Da...

Rundunar ‘Yan Sandan ihar Zamfara Na Samun Nasara A Yakin Da Take Da ‘Yan Ta’addan

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce masu kwarmatawa ‘yan ta’adda bayanan sirri sune matsalar rashin tsaron jihar kuma a sannu hukumar na samun nasarar kakkabe su.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar SP Muhammad Shehu ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da wakilin jaridar PRNigeria Hausa ta wayar tarho a safiyar juma’a.

kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar SP Muhammad Shehu ya bayyana cewa hukumar na samun gagarumar nasara a yakin da suke da ta’addanci a jihar.

“Akwai wadanda ake kira masu kwarmata bayanan sirri ga ‘yan bindiga, suna daga cikin masu bamu matsala”.

“Amma bisa hadin gwuiwar jami’an rundunar yan sanda da Al’ummar gari, wadanda ke son taimakawa  muna Aiki da su ka’in da na’in wajen zakulo  wadannan bata garin mutane domin kama su a gurfanar da su gaban kotu”

“Irin wadannan mutane mun kama su da yawa mun kuma gurfanar da su gaban kotu, yanzu haka an kai su gidan gyaran hali.

Daga bisani ya bayyana cewa a wajen hukumar ‘yan sanda masu bayyana wa ‘yan ta’adda bayanan sirri, sun fi ‘yan bindigar laifi kasancewa suke bayyana musu inda ya kamata su kai hari da yadda zasu yi garkuwa da mutane.

“suke bayyanawa wadannan bata gari rahoto akan wanda ya kamata a sace, inda ya kamata su kai hari wurin da ya kamata a ka hari kaga kuwa sune ya kamata a kawar da su daga cikin Al’umma”. In Ji shi.

Wannan dai na zuwa ne  bayan samun labarin dake cewa ‘yan bindiagr da suka yi garkuwa da masu sana’ar sayar da waya a kan hanyar su ta komawa jihar Zamfara dake arewacin Nijeriya.

Duk da cewa labarin bai baina ko an biya kudin fansa ba ko akasin haka, ko da yake an rawaito cewa sai da ‘yan bindigar suka musu dukan kawo wuka kafin sakin su.

jihar Zamfara dai na guda cikin jihohin dake Arewa maso Yammacin kasar dake fama da matsalar rashin tsaro.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp