Home General Shalkwatar Tsaron Nijeriya (DHQ)  Ta Sami Nasarar Cafke Maharan Cocin Garin Owo...

Shalkwatar Tsaron Nijeriya (DHQ)  Ta Sami Nasarar Cafke Maharan Cocin Garin Owo a Jihar Ondo.

Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Najeriya, Manjo-Janar Lucky Irabor ne ya bayyana hakan a yayin wani taron tattaunawa da shugabannin kafafen yada labarai a shalkwatar tsaron da ke Abuja.

Manjo-Janar Irabor ya ce sojoji sun kama wadanda ake zargin ne tare da hadin gwiwar wasu hukumomin tsaro.

Idan za’a iya tunawa a ranar Lahadi 5 ga watan Yuni PRNigeria ta ruwaito cewa wasu ’yan bindiga sunyi dira mikiya cocin St. Francis Xavier da ke garin Owo a jihar Ondo dake Kudu maso Yammacin Najeriya.

Nan kuma babu bata lokaci suka buda wuta kan masu ibada inda suka kashe mutum 40 tare da jikkata wasu da dama.

Wannan lamari ya tayar da ya mutsi a tsakanin mabiya addinai, inda kowane bangare ke tayar da jijiyoyin wuya a kokarin kare addininsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp