Home General Masu Garkuwa Da Suka Yi Garkuwa Da Wata Mata A Legas Sun...

Masu Garkuwa Da Suka Yi Garkuwa Da Wata Mata A Legas Sun Nemi Fansan Miliyan 10

‘Yan bindigar da sukayi garkuwa da wata mata a garin Legas sun tuntubi ‘yan uwan ta, in da suka bukaci a biya su fansar naira Miliyan 10.

An ruwaito cewa masu garkuwar da su kayi badda bami matsayin masu sayen kaya a babban kantin dake unguwar Plywood ta Epe da misalign karfe 10:07Pm sun bayyana cewa suna bukatar sayen ruwa ne kamar yadda mijinta ya bayyana wanda yace suna tare a kantin.

Sai dai ana tsaka da hada-hadar cinikayya a kantin ne kawai hasken lantarki ya dauki abinda ya kai ga ‘yan bindigar sun amshe wayoyin ma’auratan baya ga lakada musu dukan kawo wuka.

Daga bisani kuma suka rufe mijin matar a kantin suka kuma yi awon gaba da matar da nufin yin garkuwa da ita.

Wani dan uwan wadda aka yi garkuwar da ya nemi a sakaye sunan sa, ya bayyana cewa masu garkuwar sun kira mijin matar inda suka bukaci ya biya naira Miliyan 50 matsayn fansar matar sa.

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta bakin kakakin ta SP Hudenyin ta tabbatar da faruwar lamarin, inda tace tana bincike domin tabbatar da an kubutar da matar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp