Home General Masu Garkuwa Da Suka Yi Garkuwa Da Wata Mata A Legas Sun...

Masu Garkuwa Da Suka Yi Garkuwa Da Wata Mata A Legas Sun Nemi Fansan Miliyan 10

‘Yan bindigar da sukayi garkuwa da wata mata a garin Legas sun tuntubi ‘yan uwan ta, in da suka bukaci a biya su fansar naira Miliyan 10.

An ruwaito cewa masu garkuwar da su kayi badda bami matsayin masu sayen kaya a babban kantin dake unguwar Plywood ta Epe da misalign karfe 10:07Pm sun bayyana cewa suna bukatar sayen ruwa ne kamar yadda mijinta ya bayyana wanda yace suna tare a kantin.

Sai dai ana tsaka da hada-hadar cinikayya a kantin ne kawai hasken lantarki ya dauki abinda ya kai ga ‘yan bindigar sun amshe wayoyin ma’auratan baya ga lakada musu dukan kawo wuka.

Daga bisani kuma suka rufe mijin matar a kantin suka kuma yi awon gaba da matar da nufin yin garkuwa da ita.

Wani dan uwan wadda aka yi garkuwar da ya nemi a sakaye sunan sa, ya bayyana cewa masu garkuwar sun kira mijin matar inda suka bukaci ya biya naira Miliyan 50 matsayn fansar matar sa.

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta bakin kakakin ta SP Hudenyin ta tabbatar da faruwar lamarin, inda tace tana bincike domin tabbatar da an kubutar da matar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp