Home Labarai Gwamnatin Nijeriya Tace Ba za tayi Amfani Da Karfi Ba Wajen Karbo...

Gwamnatin Nijeriya Tace Ba za tayi Amfani Da Karfi Ba Wajen Karbo Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja Zuwa Kaduna Ba

Fadar shugaban kasa tace ‘yan ta’addan da suka yi garkuwa da jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna sun yaudari Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta hanyar gaza cika Alkawarin da suka dauka duk da cewa gwamnatin tarayya ta biya musu bukatun su.
Mai Magana da yawun shugaban kasar Garba Shehu ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai.
Garba Shehu yace gwamnatin tarayya ta cika wa jagoran ‘yan ta’addan Alkawarin data dauka na sakin matar sa dake da ciki, amma daga bisani ya karya Alkawarin daya dauka.
Lokacin da suke tattaunawar sulhu da Gwamnatin tarayya, sun yi alkawarin sakin fasinjojin jirgin da suka yi garkuwa dasu amma masu garkuwar sun gaza cika Alkawarin da suka dauka.
Garba shehu yace bayan gwamantin tarayya ta sauki alkawarin data dauka daga bangaren ta, su kuma ‘yan bindigar suka zo da wani sabon salon yaudara.
Wannan dai na zuwa ne sa’oi kadan bayan da shugabanin Nijeriya Muhammadu Buhari ya gana da fasinjojin da ‘yan bindigar suka sako a fadar gwamnatin tarayya a ranar Alhamis.
Garba shehu ya kara da cewa ba wannan karon farko da ‘yan ta’addan ke saba alkawarin da suka dauka ba, amma wannan ne karon farko da gwamnatin tarayya ta bayyana abinda ke faruwa ga Al’ummar kasa tsakanin ta da ‘yan bindigar.
Yanzu haka dai akwai sauran fasinjoji 31 da suka rage a hannun ‘yan ta’addan a daji, amma gwamnatin tarayyar tace baza tayi amfani da karfin tuwo ba domin karbo su, saboda tana bukatar karbo su a raye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp