Home Labarai Gwamnatin Nijeriya Tace Ba za tayi Amfani Da Karfi Ba Wajen Karbo...

Gwamnatin Nijeriya Tace Ba za tayi Amfani Da Karfi Ba Wajen Karbo Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja Zuwa Kaduna Ba

Fadar shugaban kasa tace ‘yan ta’addan da suka yi garkuwa da jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna sun yaudari Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta hanyar gaza cika Alkawarin da suka dauka duk da cewa gwamnatin tarayya ta biya musu bukatun su.
Mai Magana da yawun shugaban kasar Garba Shehu ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai.
Garba Shehu yace gwamnatin tarayya ta cika wa jagoran ‘yan ta’addan Alkawarin data dauka na sakin matar sa dake da ciki, amma daga bisani ya karya Alkawarin daya dauka.
Lokacin da suke tattaunawar sulhu da Gwamnatin tarayya, sun yi alkawarin sakin fasinjojin jirgin da suka yi garkuwa dasu amma masu garkuwar sun gaza cika Alkawarin da suka dauka.
Garba shehu yace bayan gwamantin tarayya ta sauki alkawarin data dauka daga bangaren ta, su kuma ‘yan bindigar suka zo da wani sabon salon yaudara.
Wannan dai na zuwa ne sa’oi kadan bayan da shugabanin Nijeriya Muhammadu Buhari ya gana da fasinjojin da ‘yan bindigar suka sako a fadar gwamnatin tarayya a ranar Alhamis.
Garba shehu ya kara da cewa ba wannan karon farko da ‘yan ta’addan ke saba alkawarin da suka dauka ba, amma wannan ne karon farko da gwamnatin tarayya ta bayyana abinda ke faruwa ga Al’ummar kasa tsakanin ta da ‘yan bindigar.
Yanzu haka dai akwai sauran fasinjoji 31 da suka rage a hannun ‘yan ta’addan a daji, amma gwamnatin tarayyar tace baza tayi amfani da karfin tuwo ba domin karbo su, saboda tana bukatar karbo su a raye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp