Home Labarai Gwamnatin Nijeriya Tace Ba za tayi Amfani Da Karfi Ba Wajen Karbo...

Gwamnatin Nijeriya Tace Ba za tayi Amfani Da Karfi Ba Wajen Karbo Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja Zuwa Kaduna Ba

Fadar shugaban kasa tace ‘yan ta’addan da suka yi garkuwa da jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna sun yaudari Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta hanyar gaza cika Alkawarin da suka dauka duk da cewa gwamnatin tarayya ta biya musu bukatun su.
Mai Magana da yawun shugaban kasar Garba Shehu ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai.
Garba Shehu yace gwamnatin tarayya ta cika wa jagoran ‘yan ta’addan Alkawarin data dauka na sakin matar sa dake da ciki, amma daga bisani ya karya Alkawarin daya dauka.
Lokacin da suke tattaunawar sulhu da Gwamnatin tarayya, sun yi alkawarin sakin fasinjojin jirgin da suka yi garkuwa dasu amma masu garkuwar sun gaza cika Alkawarin da suka dauka.
Garba shehu yace bayan gwamantin tarayya ta sauki alkawarin data dauka daga bangaren ta, su kuma ‘yan bindigar suka zo da wani sabon salon yaudara.
Wannan dai na zuwa ne sa’oi kadan bayan da shugabanin Nijeriya Muhammadu Buhari ya gana da fasinjojin da ‘yan bindigar suka sako a fadar gwamnatin tarayya a ranar Alhamis.
Garba shehu ya kara da cewa ba wannan karon farko da ‘yan ta’addan ke saba alkawarin da suka dauka ba, amma wannan ne karon farko da gwamnatin tarayya ta bayyana abinda ke faruwa ga Al’ummar kasa tsakanin ta da ‘yan bindigar.
Yanzu haka dai akwai sauran fasinjoji 31 da suka rage a hannun ‘yan ta’addan a daji, amma gwamnatin tarayyar tace baza tayi amfani da karfin tuwo ba domin karbo su, saboda tana bukatar karbo su a raye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp