Home General Dakarun Sojin Nijeriya Sun Halaka Manyan Kwamandojin Kungiyar Boko Haram A Kasar

Dakarun Sojin Nijeriya Sun Halaka Manyan Kwamandojin Kungiyar Boko Haram A Kasar

shalkwatar tsaron Najeriya DHQ ta bayyana cewa dakarunta sun kashe wasu manyan kwamandojin kungiyar Boko Haram cikin makwanni biyu da suka gabata.

A wani taron manema labarai a Abuja ranar Alhamis, rundunar tsaron ta ce dakarun Operation Hadin Kai ne suka kashe kwamandojin ta hanyar yi musu ruwan bama-bamai a maɓoyarsu.

Hedikwatar tsaron ta ce dakarun sun kuma halaka sama da ‘yan ta’adda 57 a wurare daban-daban bayan samame da suka kai tsakanin ranakun 11 zuwa 25 ga watan Agusta a yankin arewa maso gabashin kasar.

Shugaban sashen harkokin yaɗa labarai na rundunar, Manjo Janar Musa Danmadami, ya bayyana cewa samamen sun kunshi wanda aka yi ta sama da kasa a kan maboyar mayakan na Boko Haram da na ISWAP a jihohin Borno da Yobe.

Danmadami ya ce daya daga cikin kwamandojin da aka kashe shi ne Uzaifa, wanda yake cikin manyan jagororin kungiyar hudu.

Ya kara da cewa an kama mutum takwas da ake zargi na aikata ta’addanci da kuma hudu da ke kai wa ‘yan bindiga makamai, inda aka ceto fararen hula hudu.

A cewarsa, ‘yan Boko Haram aƙalla 1,652 da iyalansu ne suka mika wuya ga dakarun Najeriya a wurare daban-daban a baya-baya nan. Daga cikinsu akwai maza 320 da mata 442, sai kuma yara 890.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp