Home General Dakarun Sojin Nijeriya Sun Halaka Manyan Kwamandojin Kungiyar Boko Haram A Kasar

Dakarun Sojin Nijeriya Sun Halaka Manyan Kwamandojin Kungiyar Boko Haram A Kasar

shalkwatar tsaron Najeriya DHQ ta bayyana cewa dakarunta sun kashe wasu manyan kwamandojin kungiyar Boko Haram cikin makwanni biyu da suka gabata.

A wani taron manema labarai a Abuja ranar Alhamis, rundunar tsaron ta ce dakarun Operation Hadin Kai ne suka kashe kwamandojin ta hanyar yi musu ruwan bama-bamai a maɓoyarsu.

Hedikwatar tsaron ta ce dakarun sun kuma halaka sama da ‘yan ta’adda 57 a wurare daban-daban bayan samame da suka kai tsakanin ranakun 11 zuwa 25 ga watan Agusta a yankin arewa maso gabashin kasar.

Shugaban sashen harkokin yaɗa labarai na rundunar, Manjo Janar Musa Danmadami, ya bayyana cewa samamen sun kunshi wanda aka yi ta sama da kasa a kan maboyar mayakan na Boko Haram da na ISWAP a jihohin Borno da Yobe.

Danmadami ya ce daya daga cikin kwamandojin da aka kashe shi ne Uzaifa, wanda yake cikin manyan jagororin kungiyar hudu.

Ya kara da cewa an kama mutum takwas da ake zargi na aikata ta’addanci da kuma hudu da ke kai wa ‘yan bindiga makamai, inda aka ceto fararen hula hudu.

A cewarsa, ‘yan Boko Haram aƙalla 1,652 da iyalansu ne suka mika wuya ga dakarun Najeriya a wurare daban-daban a baya-baya nan. Daga cikinsu akwai maza 320 da mata 442, sai kuma yara 890.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp