Home General Dakarun Sojin Nijeriya Sun Halaka Manyan Kwamandojin Kungiyar Boko Haram A Kasar

Dakarun Sojin Nijeriya Sun Halaka Manyan Kwamandojin Kungiyar Boko Haram A Kasar

shalkwatar tsaron Najeriya DHQ ta bayyana cewa dakarunta sun kashe wasu manyan kwamandojin kungiyar Boko Haram cikin makwanni biyu da suka gabata.

A wani taron manema labarai a Abuja ranar Alhamis, rundunar tsaron ta ce dakarun Operation Hadin Kai ne suka kashe kwamandojin ta hanyar yi musu ruwan bama-bamai a maɓoyarsu.

Hedikwatar tsaron ta ce dakarun sun kuma halaka sama da ‘yan ta’adda 57 a wurare daban-daban bayan samame da suka kai tsakanin ranakun 11 zuwa 25 ga watan Agusta a yankin arewa maso gabashin kasar.

Shugaban sashen harkokin yaɗa labarai na rundunar, Manjo Janar Musa Danmadami, ya bayyana cewa samamen sun kunshi wanda aka yi ta sama da kasa a kan maboyar mayakan na Boko Haram da na ISWAP a jihohin Borno da Yobe.

Danmadami ya ce daya daga cikin kwamandojin da aka kashe shi ne Uzaifa, wanda yake cikin manyan jagororin kungiyar hudu.

Ya kara da cewa an kama mutum takwas da ake zargi na aikata ta’addanci da kuma hudu da ke kai wa ‘yan bindiga makamai, inda aka ceto fararen hula hudu.

A cewarsa, ‘yan Boko Haram aƙalla 1,652 da iyalansu ne suka mika wuya ga dakarun Najeriya a wurare daban-daban a baya-baya nan. Daga cikinsu akwai maza 320 da mata 442, sai kuma yara 890.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp