Home Labarai Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da...

Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da shi

Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da shi

 

Wani basaraken gargajiya na kauyen Pinau da ke karamar hukumar Wase a jihar Filato, Dokta Dadda’u Ahmad, wanda aka yi garkuwa da shi da sanyin safiyar Talata tare da direbansa, sojojin da ke aiki da rundunar ‘Operation Safe Haven’ a kauyen sun ceto shi.

Kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Filato da Bauchi da wasu sassan Karina Manjo Ishaku Takwa ya tabbatar da faruwar lamarin.

Wani mazaunin kauyen Hassan Pinau ya ce, wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da basaraken gargajiya da aka ceto tare da direbansa a hanyarsu ta zuwa Wase.

Ya bayyana cewa jim kadan bayan samun labarin faruwar lamarin ga sojoji a kauyen, sai suka zage damtse tare da bin diddigin masu garkuwa da mutanen inda suka kwato bindigogi biyu, da babura uku.

Musa Hassan, wani ma’aikacin da ke kula da unguwanni a yankin, ya shaida wa jaridar The Nation cewa: “Ina tare da sojoji a lokacin aikin ceto. Sojoji da wasu ’yan unguwar ne suka dawo da basaraken gargajiyar kauyen da suka yi awon gaba da masu garkuwa da mutane zuwa daji.“Kowa yana farin ciki a ƙauyen yanzu. An yi musayar wuta tsakanin sojoji da maharan kafin a ceto wadanda abin ya shafa.

“Sojoji sun yi kokari. Muna rokon Allah Ya ba su ikon ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da suke yi.”

Source: The Nation

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. Shuaib
X whatsapp