Home Labarai Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da...

Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da shi

Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da shi

 

Wani basaraken gargajiya na kauyen Pinau da ke karamar hukumar Wase a jihar Filato, Dokta Dadda’u Ahmad, wanda aka yi garkuwa da shi da sanyin safiyar Talata tare da direbansa, sojojin da ke aiki da rundunar ‘Operation Safe Haven’ a kauyen sun ceto shi.

Kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Filato da Bauchi da wasu sassan Karina Manjo Ishaku Takwa ya tabbatar da faruwar lamarin.

Wani mazaunin kauyen Hassan Pinau ya ce, wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da basaraken gargajiya da aka ceto tare da direbansa a hanyarsu ta zuwa Wase.

Ya bayyana cewa jim kadan bayan samun labarin faruwar lamarin ga sojoji a kauyen, sai suka zage damtse tare da bin diddigin masu garkuwa da mutanen inda suka kwato bindigogi biyu, da babura uku.

Musa Hassan, wani ma’aikacin da ke kula da unguwanni a yankin, ya shaida wa jaridar The Nation cewa: “Ina tare da sojoji a lokacin aikin ceto. Sojoji da wasu ’yan unguwar ne suka dawo da basaraken gargajiyar kauyen da suka yi awon gaba da masu garkuwa da mutane zuwa daji.“Kowa yana farin ciki a ƙauyen yanzu. An yi musayar wuta tsakanin sojoji da maharan kafin a ceto wadanda abin ya shafa.

“Sojoji sun yi kokari. Muna rokon Allah Ya ba su ikon ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da suke yi.”

Source: The Nation

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp