Home SIYASA Sabuwar Firaministan Burtaniya ta Nada ‘Yar Najeriya a Matsayin Mamba a Majalisar...

Sabuwar Firaministan Burtaniya ta Nada ‘Yar Najeriya a Matsayin Mamba a Majalisar Ministoci

Sabuwar Firaministan Burtaniya ta Nada ‘Yar Najeriya a Matsayin Mamba a Majalisar Ministoci

 

By Ozumi Abdul-Satumba 7, 2022

Kemi Badenoch

LABARIN SIYASA- Sabuwar Firaministan Burtaniya, Liz Truss ta nada wata ‘yar siyasa ‘yar asalin Najeriya, Kemi Badenoch, a matsayin mamba a sabuwar majalisar ministocinta da aka yi wa garambawul a ranar Talata.

An nada Kemi a matsayin sabuwar sakatariyar kasuwancin kasa da kasa kuma shugabar hukumar kasuwanci.

Nadin, wanda ke kunshe a cikin wani sakon twitter da aka buga a tabbataccen shafin Twitter na Firayim Ministan Burtaniya, @10DowningStreet ranar Talata ya karanta:

“An nada Kemi Badenoch MP @KemiBadenoch Sakatariyar Harkokin Ciniki ta Kasa da Kasa kuma Shugabar Hukumar Kasuwanci @TradeGovUK.”

Da take amincewa da nadin, Kemi ta yi amfani da tabbataccen shafinta na Twitter inda ta bayyana jin dadin ta da nadin.

Babbar mamba ta jam’iyyar Conservative ta ce ba za ta iya jira ta yi cikakken amfani da damar Biritaniya don samar da karin ayyuka da damammaki ba.

“Na yi farin cikin fara sabon aiki na a @tradegovuk! Muna sa ran fitar da cikakken damar Duniyar Burtaniya ta yadda za mu iya samar da karin ayyukan yi, karin ci gaba da karin damammaki a fadin Burtaniya, ”in ji ta.

A baya Kemi Badenoch ta taba rike mukamin karamar ministar kananan hukumomi da imani da al’ummomi da kuma karamar ministar daidaito.

Kemi Badenoch, wacce ita ma ta tsaya takarar shugaban jam’iyyar Conservative, Rishi Sunak, Penny Mordaunt, da Liz Truss, da ta lashe zaben, ta fice daga takarar neman zama sabon Firaminista.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp