Home SIYASA Sabuwar Firaministan Burtaniya ta Nada ‘Yar Najeriya a Matsayin Mamba a Majalisar...

Sabuwar Firaministan Burtaniya ta Nada ‘Yar Najeriya a Matsayin Mamba a Majalisar Ministoci

Sabuwar Firaministan Burtaniya ta Nada ‘Yar Najeriya a Matsayin Mamba a Majalisar Ministoci

 

By Ozumi Abdul-Satumba 7, 2022

Kemi Badenoch

LABARIN SIYASA- Sabuwar Firaministan Burtaniya, Liz Truss ta nada wata ‘yar siyasa ‘yar asalin Najeriya, Kemi Badenoch, a matsayin mamba a sabuwar majalisar ministocinta da aka yi wa garambawul a ranar Talata.

An nada Kemi a matsayin sabuwar sakatariyar kasuwancin kasa da kasa kuma shugabar hukumar kasuwanci.

Nadin, wanda ke kunshe a cikin wani sakon twitter da aka buga a tabbataccen shafin Twitter na Firayim Ministan Burtaniya, @10DowningStreet ranar Talata ya karanta:

“An nada Kemi Badenoch MP @KemiBadenoch Sakatariyar Harkokin Ciniki ta Kasa da Kasa kuma Shugabar Hukumar Kasuwanci @TradeGovUK.”

Da take amincewa da nadin, Kemi ta yi amfani da tabbataccen shafinta na Twitter inda ta bayyana jin dadin ta da nadin.

Babbar mamba ta jam’iyyar Conservative ta ce ba za ta iya jira ta yi cikakken amfani da damar Biritaniya don samar da karin ayyuka da damammaki ba.

“Na yi farin cikin fara sabon aiki na a @tradegovuk! Muna sa ran fitar da cikakken damar Duniyar Burtaniya ta yadda za mu iya samar da karin ayyukan yi, karin ci gaba da karin damammaki a fadin Burtaniya, ”in ji ta.

A baya Kemi Badenoch ta taba rike mukamin karamar ministar kananan hukumomi da imani da al’ummomi da kuma karamar ministar daidaito.

Kemi Badenoch, wacce ita ma ta tsaya takarar shugaban jam’iyyar Conservative, Rishi Sunak, Penny Mordaunt, da Liz Truss, da ta lashe zaben, ta fice daga takarar neman zama sabon Firaminista.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp