Home SIYASA PDP: Ayu ya Mika wa Mataimakin sa Shugabancin Jam’iyyar

PDP: Ayu ya Mika wa Mataimakin sa Shugabancin Jam’iyyar

PDP: Ayu ya Mika wa Mataimakin sa Shugabancin Jam’iyyar

 

Daga Ozumi Abdul

SIYASA – Shugaban jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) na kasa, Dr. Iyorchia Ayu, ya tashi daga kasar zuwa Turai, yayin da gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya kara jaddada kiransa na yin murabus.

Ayu ya mikawa mataimakin shugaban jam’iyyar (Arewa), Iliya Damagun, wanda zai ci gaba da tafiyar da jam’iyyar a matsayin shugaban riko.

Wannan na zuwa ne a wata sanarwa da mai ba da shawara na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa na Ayu, Simon Imobo-Tswam, ya fitar a ranar Talata.

Sanarwar ta ce: “Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Dr. Iyorchia Ayu, zai bar Najeriya zuwa Turai gobe Laraba.

“Ayu zai yi waje da kasar na kusan makonni biyu. Yayin da ya tafi, Mataimakin Shugaban (Arewa), Iliya Damagun, zai yi aiki a madadinsa.

“Tuni shugaban kasa ya mika takardar mika mulki ga hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta.

Ana sa ran zai dawo a karshen wata.”

Gwamna Wike da sansaninsa a cikin jam’iyyar PDP sun yi ta kiraye-kirayen murabus din Ayu bisa ga alkawarin da ya yi wa ‘yan jam’iyyar na cewa idan dan Arewa ya fito takarar shugaban kasa zai yi murabus.

Sai dai a kwanakin baya Ayu ya ce ba zai sauka ba, yana mai cewa irin su Wike da ke kiran kan sa yara ne da ba su nan a lokacin da aka kafa jam’iyyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp