Home SIYASA Gwamna Bello ya Jajantawa Wadanda Fashewar Tankar Mai ta Shafa

Gwamna Bello ya Jajantawa Wadanda Fashewar Tankar Mai ta Shafa

Gwamna Bello ya Jajantawa Wadanda Fashewar Tankar Mai ta Shafa

 

SIYASA – Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bayyana kaduwarsa dangane da mumunar fashewar tankar tanka da ta yi sanadin mutuwar wasu mutane a Ochinobi dake karamar hukumar Ankpa a jihar ranar Laraba.

Gwamna Bello a wata sanarwa dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran sa, Onogwu Mohammed, ya kuma jajantawa iyalan wadanda suka mutu a wannan mummunan lamari.

Yayin da yake addu’ar Allah ya baiwa wadanda suka rasu a huta lafiya, Bello ya kuma yi addu’ar samun sauki da lafiya ga wadanda suka tsira daga wannan lamari.

Gwamnan ya bayyana abin da ya faru a Ankpa a matsayin wani abin takaici, ya kuma yaba da kokarin da gwamnatin karamar hukumar Ankpa da hukumar bada agajin gaggawa ta jihar suka yi wajen gano bakin zaren lamarin domin kaucewa afkuwar irin haka nan gaba kadan.

Yayin da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar da sauran hukumomin da abin ya shafa suka kasance a wurin domin shawo kan lamarin, Gwamnan ya kuma kafa wakilan gwamnati masu karfi da za su ziyarci yankin a ranar Juma’a.

Gwamna Bello ya bukaci direbobin kera motoci da su tabbatar da cewa motocin na su na cikin ingantattun injina kafin su afka kan tituna domin gujewa jefa jihar da kasa cikin masifun da fashewar tanka ta haifar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp