Home SIYASA Tinubu ba ya Nan Yayin Da ‘Yan Takarar Shugaban Kasa sun Shirya...

Tinubu ba ya Nan Yayin Da ‘Yan Takarar Shugaban Kasa sun Shirya Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya

Tinubu ba ya Nan Yayin Da ‘Yan Takarar Shugaban Kasa sun Shirya Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya

 

SIYASA – Wasu ‘yan takarar shugaban kasa da shugabannin jam’iyyun siyasa 18 da suka yi wa rajista sun fara isa cibiyar taron kasa da kasa (ICC) domin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ta kasa gabanin babban zabe na 2023.

Kwamitin zaman lafiya na kasa karkashin jagorancin tsohon shugaban kasa Janar Abdulsalami Abubakar da Bishop Matthew Hassan Kukah ne suka shirya taron.

An kirkiro shirin ne a shekarar 2014 domin mayar da martani ga barazanar da ke kunno kai a babban zaben shekarar 2015.

‘Yan takarar da suka halarci bikin da ake shirin farawa sun hada da dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) Sanata Kashim Shettima wanda ke wakiltar abokin takararsa, Bola Ahmed Tinubu; ‘Yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Action Alliance (AA) Omoleye Sowore da takwaransa na jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP), Sanata Rabiu Kwanwaso.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullah Adamu, shi ma yana kan kujerar domin gudanar da taron.

Cikakkun bayanai anjima…

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp