Home Labarai Sojoji sun Dakile Harin Gamboru Ngala, sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19

Sojoji sun Dakile Harin Gamboru Ngala, sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19

A kalla mayakan kungiyar tada kayar baya ta boko haram tsagin ISWAP 19 ne suka halaka sakamakon wani barin wuta da dakarun soji karkashin rundunar Operation HADIN KAI suka kai a garin Gamborun Ngala dake jihar Borno a arewa maso gabashin Nijeriya.

An ruwaito cewa dakarun hadin gwuiw na (CJTF) ne suka kai hari a ranar 11 ga watan Oktoba, a kokarin su na dakile wani harin kwanton bauna da ‘yan ta’addan suka shirya kai wa sojoji yayin da suke tsaka da sintiri wani bangare na kakkabe bata garin.

Garin Gamboru, dake iyakar Nijeriya, wanda ke da tazarar kilomita 80 daga Maiduguri babban birnin jihar ta Borno.

Wata majiyar asiri ta shaidawa Zagazola Makama, wani kwararre kan yaki da ta’addanci a yankin tafkin chadi cewa ‘yan ta’addan sun kawo harin ne kan Babura wasu kuma kan motoci kirar Hilux dauke da bindigu, inda suka fara kai harin kan sojojin.

Majiyar tace sojojin basu yi wata wat aba suka mayar da kora, ta hanyar dakile kokarin da ‘yan bindigar abinda ya dauki tsahon mintuna 40 ana musayar wuta.

Sai dai daga bisani dakrun sojojin sun sami galaba kan ‘yan bindiga, inda suka tilasta musu hakura da kudirin da suka dauka domin tsare.

Dakarun sojin sun sami nasarar kwace wata babbar bindiga bayan sun halaka dukkan wadanda ke dauke da ita, inda suka sami damar kwace Babura 9 da wasu tarin makamai wanda suka hada da PKT, AK-47 guda 9 dare da tarin Alburusai.

Sai dai yace babu wani rahoton mutuwa daga bangaren sojojin, amma mutum biyu sun sami raunika.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp