Home Labarai Sojoji sun Dakile Harin Gamboru Ngala, sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19

Sojoji sun Dakile Harin Gamboru Ngala, sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19

A kalla mayakan kungiyar tada kayar baya ta boko haram tsagin ISWAP 19 ne suka halaka sakamakon wani barin wuta da dakarun soji karkashin rundunar Operation HADIN KAI suka kai a garin Gamborun Ngala dake jihar Borno a arewa maso gabashin Nijeriya.

An ruwaito cewa dakarun hadin gwuiw na (CJTF) ne suka kai hari a ranar 11 ga watan Oktoba, a kokarin su na dakile wani harin kwanton bauna da ‘yan ta’addan suka shirya kai wa sojoji yayin da suke tsaka da sintiri wani bangare na kakkabe bata garin.

Garin Gamboru, dake iyakar Nijeriya, wanda ke da tazarar kilomita 80 daga Maiduguri babban birnin jihar ta Borno.

Wata majiyar asiri ta shaidawa Zagazola Makama, wani kwararre kan yaki da ta’addanci a yankin tafkin chadi cewa ‘yan ta’addan sun kawo harin ne kan Babura wasu kuma kan motoci kirar Hilux dauke da bindigu, inda suka fara kai harin kan sojojin.

Majiyar tace sojojin basu yi wata wat aba suka mayar da kora, ta hanyar dakile kokarin da ‘yan bindigar abinda ya dauki tsahon mintuna 40 ana musayar wuta.

Sai dai daga bisani dakrun sojojin sun sami galaba kan ‘yan bindiga, inda suka tilasta musu hakura da kudirin da suka dauka domin tsare.

Dakarun sojin sun sami nasarar kwace wata babbar bindiga bayan sun halaka dukkan wadanda ke dauke da ita, inda suka sami damar kwace Babura 9 da wasu tarin makamai wanda suka hada da PKT, AK-47 guda 9 dare da tarin Alburusai.

Sai dai yace babu wani rahoton mutuwa daga bangaren sojojin, amma mutum biyu sun sami raunika.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp