Home Labarai Sojoji sun Dakile Harin Gamboru Ngala, sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19

Sojoji sun Dakile Harin Gamboru Ngala, sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19

A kalla mayakan kungiyar tada kayar baya ta boko haram tsagin ISWAP 19 ne suka halaka sakamakon wani barin wuta da dakarun soji karkashin rundunar Operation HADIN KAI suka kai a garin Gamborun Ngala dake jihar Borno a arewa maso gabashin Nijeriya.

An ruwaito cewa dakarun hadin gwuiw na (CJTF) ne suka kai hari a ranar 11 ga watan Oktoba, a kokarin su na dakile wani harin kwanton bauna da ‘yan ta’addan suka shirya kai wa sojoji yayin da suke tsaka da sintiri wani bangare na kakkabe bata garin.

Garin Gamboru, dake iyakar Nijeriya, wanda ke da tazarar kilomita 80 daga Maiduguri babban birnin jihar ta Borno.

Wata majiyar asiri ta shaidawa Zagazola Makama, wani kwararre kan yaki da ta’addanci a yankin tafkin chadi cewa ‘yan ta’addan sun kawo harin ne kan Babura wasu kuma kan motoci kirar Hilux dauke da bindigu, inda suka fara kai harin kan sojojin.

Majiyar tace sojojin basu yi wata wat aba suka mayar da kora, ta hanyar dakile kokarin da ‘yan bindigar abinda ya dauki tsahon mintuna 40 ana musayar wuta.

Sai dai daga bisani dakrun sojojin sun sami galaba kan ‘yan bindiga, inda suka tilasta musu hakura da kudirin da suka dauka domin tsare.

Dakarun sojin sun sami nasarar kwace wata babbar bindiga bayan sun halaka dukkan wadanda ke dauke da ita, inda suka sami damar kwace Babura 9 da wasu tarin makamai wanda suka hada da PKT, AK-47 guda 9 dare da tarin Alburusai.

Sai dai yace babu wani rahoton mutuwa daga bangaren sojojin, amma mutum biyu sun sami raunika.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp