Home SIYASA Buhari ya Rantsar da Mai shari’a Ariwoola a Matsayin Babban CJN

Buhari ya Rantsar da Mai shari’a Ariwoola a Matsayin Babban CJN

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da Justice Olukayode Ariwoola a matsayin babban alkalin alkalan Najeriya (CJN).

Bikin rantsuwar da ya gudana gabanin fara taron majalisar zartarwa ta tarayya na mako, (FEC), ya samu halartar mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, da gwamnonin jihohin Oyo da Ondo, Seyi Makinde da Rotimi Akeredolu.

sai kuma Sauran alkalan kotun kolin Najeriya wadanda a matsayin wadanda suka halarci bikin; Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Boss Mustapha; Shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Dr Folasade Yemi-Esan; Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno (Rtd).

Sauran sun hadar da ministocin da suka shigo domin halartar taron majalisar na mako, ciki har da Hadi Sirika (Aviation); Olorunnimbe Mamora (Kimiyya, Fasaha); Chris Ngige (Kwadago da Nagartar Aiki); Abubakar Malami (Ministan shari’a, Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya); Niyi Adebayo (Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari); Babatunde Fashola (Ayyuka da Gidaje); Abubakar Aliyu (Makamashi) da sauransu.

Da yake zantawa da manema labarai bayan rantsar da shi, Mai shari’a Ariwoola ya yi kira ga ‘yan siyasa a kasar nan da su kyale bangaren shari’a ya yi aiki yadda ya kamata ganin yadda zaben 2023 ke gabatowa yayin da ya yi alkawarin kawo gyara a kotun koli.

A nasa bangaren, gwamna Seyi Makinde ya bayyana godiya a madadin jama’a da gwamnatin jihar Oyo ga shugaban.

A halin da ake ciki, majalisar ta yi shiru na minti daya domin karrama tsohon ministan ayyuka na musamman kuma shugaban jam’iyyar PDP, Cif Vincent Ogbulafor, wanda ya rasu kwanan nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp