Home SIYASA Buhari ya Rantsar da Mai shari’a Ariwoola a Matsayin Babban CJN

Buhari ya Rantsar da Mai shari’a Ariwoola a Matsayin Babban CJN

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da Justice Olukayode Ariwoola a matsayin babban alkalin alkalan Najeriya (CJN).

Bikin rantsuwar da ya gudana gabanin fara taron majalisar zartarwa ta tarayya na mako, (FEC), ya samu halartar mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, da gwamnonin jihohin Oyo da Ondo, Seyi Makinde da Rotimi Akeredolu.

sai kuma Sauran alkalan kotun kolin Najeriya wadanda a matsayin wadanda suka halarci bikin; Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Boss Mustapha; Shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Dr Folasade Yemi-Esan; Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno (Rtd).

Sauran sun hadar da ministocin da suka shigo domin halartar taron majalisar na mako, ciki har da Hadi Sirika (Aviation); Olorunnimbe Mamora (Kimiyya, Fasaha); Chris Ngige (Kwadago da Nagartar Aiki); Abubakar Malami (Ministan shari’a, Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya); Niyi Adebayo (Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari); Babatunde Fashola (Ayyuka da Gidaje); Abubakar Aliyu (Makamashi) da sauransu.

Da yake zantawa da manema labarai bayan rantsar da shi, Mai shari’a Ariwoola ya yi kira ga ‘yan siyasa a kasar nan da su kyale bangaren shari’a ya yi aiki yadda ya kamata ganin yadda zaben 2023 ke gabatowa yayin da ya yi alkawarin kawo gyara a kotun koli.

A nasa bangaren, gwamna Seyi Makinde ya bayyana godiya a madadin jama’a da gwamnatin jihar Oyo ga shugaban.

A halin da ake ciki, majalisar ta yi shiru na minti daya domin karrama tsohon ministan ayyuka na musamman kuma shugaban jam’iyyar PDP, Cif Vincent Ogbulafor, wanda ya rasu kwanan nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp