Home SIYASA Buhari ya Rantsar da Mai shari’a Ariwoola a Matsayin Babban CJN

Buhari ya Rantsar da Mai shari’a Ariwoola a Matsayin Babban CJN

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da Justice Olukayode Ariwoola a matsayin babban alkalin alkalan Najeriya (CJN).

Bikin rantsuwar da ya gudana gabanin fara taron majalisar zartarwa ta tarayya na mako, (FEC), ya samu halartar mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, da gwamnonin jihohin Oyo da Ondo, Seyi Makinde da Rotimi Akeredolu.

sai kuma Sauran alkalan kotun kolin Najeriya wadanda a matsayin wadanda suka halarci bikin; Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Boss Mustapha; Shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Dr Folasade Yemi-Esan; Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno (Rtd).

Sauran sun hadar da ministocin da suka shigo domin halartar taron majalisar na mako, ciki har da Hadi Sirika (Aviation); Olorunnimbe Mamora (Kimiyya, Fasaha); Chris Ngige (Kwadago da Nagartar Aiki); Abubakar Malami (Ministan shari’a, Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya); Niyi Adebayo (Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari); Babatunde Fashola (Ayyuka da Gidaje); Abubakar Aliyu (Makamashi) da sauransu.

Da yake zantawa da manema labarai bayan rantsar da shi, Mai shari’a Ariwoola ya yi kira ga ‘yan siyasa a kasar nan da su kyale bangaren shari’a ya yi aiki yadda ya kamata ganin yadda zaben 2023 ke gabatowa yayin da ya yi alkawarin kawo gyara a kotun koli.

A nasa bangaren, gwamna Seyi Makinde ya bayyana godiya a madadin jama’a da gwamnatin jihar Oyo ga shugaban.

A halin da ake ciki, majalisar ta yi shiru na minti daya domin karrama tsohon ministan ayyuka na musamman kuma shugaban jam’iyyar PDP, Cif Vincent Ogbulafor, wanda ya rasu kwanan nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp