Home Labarai Muric ta bukaci Bankin Polaris Ya nemi Afuwar Musulmin Nijeriya

Muric ta bukaci Bankin Polaris Ya nemi Afuwar Musulmin Nijeriya

Kungiyar kare hakkin musulmi ta MURIC ta bukaci mahukuntan bankin Polaris da su nemi afuwar musulmi  ba tare da bata lokaci ba, nan da kwanaki bakwai, ko kuma abukan huldar bankin musulmi su fara kauracewa banki.

Hakan na kunshe ta cikin wata sanarwa da darakta kungiyar farfesa Ishaq Akintola ya fitar aka raba ga manema labarai mai dauke da kwanan watan 14 ga watan Oktoban 2022

Wannan na zuwa ne sakamakon wani umarni dababban jami’in bankin ya yi ga ma’aikatan sa musulmi da kada su halarci taron sallar juma’a.

Sanarwa tace wata babbar Jami’a abankin na Polaris Damilola Adebara ta aikewa ma’aikatan bankin ta adreshin Email a ranar 11 ga watan 2022 da misalin 12:10 na yamma dake bada umarnin da kada su halarci taron juma’a gami da yin barazanar daukar mataki kan wanda yayi kuskuren ketare wannan doka.

Muric na Alla-wadai da kakkausar murya da wannan kudirin na kiristantar da bankin da kuma kawar da musulmin dake aiki a karkashin bankin na Polaris. wannan ke nuna rashin da’a da kuma rashin kwarewar aiki.

Daga bisani sanarwa ta gargadi bankin cewa wahaniyar sa ta kiyayi ramar musulmi, tare da umartar mahukunta dasu fito fili su nemi afuwar musulmin Nijeriya ko kuma su fara kauracewa bankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp