Home Labarai Muric ta bukaci Bankin Polaris Ya nemi Afuwar Musulmin Nijeriya

Muric ta bukaci Bankin Polaris Ya nemi Afuwar Musulmin Nijeriya

Kungiyar kare hakkin musulmi ta MURIC ta bukaci mahukuntan bankin Polaris da su nemi afuwar musulmi  ba tare da bata lokaci ba, nan da kwanaki bakwai, ko kuma abukan huldar bankin musulmi su fara kauracewa banki.

Hakan na kunshe ta cikin wata sanarwa da darakta kungiyar farfesa Ishaq Akintola ya fitar aka raba ga manema labarai mai dauke da kwanan watan 14 ga watan Oktoban 2022

Wannan na zuwa ne sakamakon wani umarni dababban jami’in bankin ya yi ga ma’aikatan sa musulmi da kada su halarci taron sallar juma’a.

Sanarwa tace wata babbar Jami’a abankin na Polaris Damilola Adebara ta aikewa ma’aikatan bankin ta adreshin Email a ranar 11 ga watan 2022 da misalin 12:10 na yamma dake bada umarnin da kada su halarci taron juma’a gami da yin barazanar daukar mataki kan wanda yayi kuskuren ketare wannan doka.

Muric na Alla-wadai da kakkausar murya da wannan kudirin na kiristantar da bankin da kuma kawar da musulmin dake aiki a karkashin bankin na Polaris. wannan ke nuna rashin da’a da kuma rashin kwarewar aiki.

Daga bisani sanarwa ta gargadi bankin cewa wahaniyar sa ta kiyayi ramar musulmi, tare da umartar mahukunta dasu fito fili su nemi afuwar musulmin Nijeriya ko kuma su fara kauracewa bankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp