Home Labarai Muric ta bukaci Bankin Polaris Ya nemi Afuwar Musulmin Nijeriya

Muric ta bukaci Bankin Polaris Ya nemi Afuwar Musulmin Nijeriya

Kungiyar kare hakkin musulmi ta MURIC ta bukaci mahukuntan bankin Polaris da su nemi afuwar musulmi  ba tare da bata lokaci ba, nan da kwanaki bakwai, ko kuma abukan huldar bankin musulmi su fara kauracewa banki.

Hakan na kunshe ta cikin wata sanarwa da darakta kungiyar farfesa Ishaq Akintola ya fitar aka raba ga manema labarai mai dauke da kwanan watan 14 ga watan Oktoban 2022

Wannan na zuwa ne sakamakon wani umarni dababban jami’in bankin ya yi ga ma’aikatan sa musulmi da kada su halarci taron sallar juma’a.

Sanarwa tace wata babbar Jami’a abankin na Polaris Damilola Adebara ta aikewa ma’aikatan bankin ta adreshin Email a ranar 11 ga watan 2022 da misalin 12:10 na yamma dake bada umarnin da kada su halarci taron juma’a gami da yin barazanar daukar mataki kan wanda yayi kuskuren ketare wannan doka.

Muric na Alla-wadai da kakkausar murya da wannan kudirin na kiristantar da bankin da kuma kawar da musulmin dake aiki a karkashin bankin na Polaris. wannan ke nuna rashin da’a da kuma rashin kwarewar aiki.

Daga bisani sanarwa ta gargadi bankin cewa wahaniyar sa ta kiyayi ramar musulmi, tare da umartar mahukunta dasu fito fili su nemi afuwar musulmin Nijeriya ko kuma su fara kauracewa bankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp