Home Labarai Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina ya Fice da APC zuwa APC

Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina ya Fice da APC zuwa APC

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina, SSG Mustapha Inuwa, ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa PDP.

Inuwa, wanda ya sha kaye a yunkurinsa na neman tikitin takarar gwamna a jam’iyyar APC, ya bayyana sauya shekar ta sa zuwa PDP ne a yau Lahadi a Katsina, yayin da ya ke jawabi ga magoya bayansa.

Ya bayyana cewa ya dauki matakin ne bayan tattaunawa da magoya bayansa a fadin jihar

Inuwa wanda ya yi aiki a matsayin SSG a gwamnatin Gwamna Aminu Masari daga 2015 har zuwa zaben fidda gwani na gwamna a watan Mayun 2022, ya yi ikirarin cewa an mayar da shi saniyar-ware a duk harkokin APC a jihar.

“Idan za a iya tunawa, a lokacin zaben fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC a jihar, mun san duk abin da ya faru a wancan lokacin, kuma a karshe an bayyana wanda ya yi nasara.

“Mun amince da shan kaye kuma mun yi alkawarin mara wa dan takarar jam’iyyar baya, bayan da ya ziyarce ni kuma na ba shi tabbacin goyon bayan da ya dace.

“Amma abin takaici, tun a wancan lokacin, ba a taba tuntuɓa ta da wata harka da ta shafi ci gaban jam’iyyar a jihar Katsina ba, wanda hakan ya sa a ka maishe mu saniyar-ware a jam’iyyar.

“Wannan alama ce karara cewa ba a ɗaukar mu a matsayin cikakkun ƴan APC, bar ta kai ga wasu ma na cewa za su iya cin zabe ko ba mu.

“Duba da wannan yanayi, mun gamsu cewa ba za mu iya jure zama a haka ba. Sabo da haka Ni da ɗaukacin magoya baya na mun sauya sheƙa zuwa PDP,” in ji shi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp