Home Labarai Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina ya Fice da APC zuwa APC

Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina ya Fice da APC zuwa APC

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina, SSG Mustapha Inuwa, ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa PDP.

Inuwa, wanda ya sha kaye a yunkurinsa na neman tikitin takarar gwamna a jam’iyyar APC, ya bayyana sauya shekar ta sa zuwa PDP ne a yau Lahadi a Katsina, yayin da ya ke jawabi ga magoya bayansa.

Ya bayyana cewa ya dauki matakin ne bayan tattaunawa da magoya bayansa a fadin jihar

Inuwa wanda ya yi aiki a matsayin SSG a gwamnatin Gwamna Aminu Masari daga 2015 har zuwa zaben fidda gwani na gwamna a watan Mayun 2022, ya yi ikirarin cewa an mayar da shi saniyar-ware a duk harkokin APC a jihar.

“Idan za a iya tunawa, a lokacin zaben fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC a jihar, mun san duk abin da ya faru a wancan lokacin, kuma a karshe an bayyana wanda ya yi nasara.

“Mun amince da shan kaye kuma mun yi alkawarin mara wa dan takarar jam’iyyar baya, bayan da ya ziyarce ni kuma na ba shi tabbacin goyon bayan da ya dace.

“Amma abin takaici, tun a wancan lokacin, ba a taba tuntuɓa ta da wata harka da ta shafi ci gaban jam’iyyar a jihar Katsina ba, wanda hakan ya sa a ka maishe mu saniyar-ware a jam’iyyar.

“Wannan alama ce karara cewa ba a ɗaukar mu a matsayin cikakkun ƴan APC, bar ta kai ga wasu ma na cewa za su iya cin zabe ko ba mu.

“Duba da wannan yanayi, mun gamsu cewa ba za mu iya jure zama a haka ba. Sabo da haka Ni da ɗaukacin magoya baya na mun sauya sheƙa zuwa PDP,” in ji shi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp