Home Labarai Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina ya Fice da APC zuwa APC

Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina ya Fice da APC zuwa APC

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina, SSG Mustapha Inuwa, ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa PDP.

Inuwa, wanda ya sha kaye a yunkurinsa na neman tikitin takarar gwamna a jam’iyyar APC, ya bayyana sauya shekar ta sa zuwa PDP ne a yau Lahadi a Katsina, yayin da ya ke jawabi ga magoya bayansa.

Ya bayyana cewa ya dauki matakin ne bayan tattaunawa da magoya bayansa a fadin jihar

Inuwa wanda ya yi aiki a matsayin SSG a gwamnatin Gwamna Aminu Masari daga 2015 har zuwa zaben fidda gwani na gwamna a watan Mayun 2022, ya yi ikirarin cewa an mayar da shi saniyar-ware a duk harkokin APC a jihar.

“Idan za a iya tunawa, a lokacin zaben fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC a jihar, mun san duk abin da ya faru a wancan lokacin, kuma a karshe an bayyana wanda ya yi nasara.

“Mun amince da shan kaye kuma mun yi alkawarin mara wa dan takarar jam’iyyar baya, bayan da ya ziyarce ni kuma na ba shi tabbacin goyon bayan da ya dace.

“Amma abin takaici, tun a wancan lokacin, ba a taba tuntuɓa ta da wata harka da ta shafi ci gaban jam’iyyar a jihar Katsina ba, wanda hakan ya sa a ka maishe mu saniyar-ware a jam’iyyar.

“Wannan alama ce karara cewa ba a ɗaukar mu a matsayin cikakkun ƴan APC, bar ta kai ga wasu ma na cewa za su iya cin zabe ko ba mu.

“Duba da wannan yanayi, mun gamsu cewa ba za mu iya jure zama a haka ba. Sabo da haka Ni da ɗaukacin magoya baya na mun sauya sheƙa zuwa PDP,” in ji shi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp