Home Labarai Gwamnatin Tarayya ta Tabbatar da Tsige Shugaban Hukumar Hidimar Kasa (NYSC)

Gwamnatin Tarayya ta Tabbatar da Tsige Shugaban Hukumar Hidimar Kasa (NYSC)

Rahotannin na bayyana cewa ministan matasa da wasannin na Nijeriya Sunday Dare ya tabbatar da tsige darakta janar na hukumar yi wa kasa hidima (NYSC birgidiya janar Muhammad Fadah

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa a daren juma’a domin tabbatar da sakon tambayar da aka yi masa kan gaskiyar labarin.

Tunda fari da jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya sallami Shugaban Hukumar kula da Matasa Ƴan yi wa ƙasa Hidima, NYSC, Muhammad Kukah Fadah, ƙasa da watanni 6 da naɗa shi.

Kawo yanzu dai babu wani dalili da a ka bayyana cewa shi ne ya sanya Buhari ya sallami Fadah, amma wata nahiyar sirri a fadar shugaban ƙasa ta shaida wa jaridar PRNigeria cewa korar ta sa ba ta rasa nasaba da rashin ƙoƙari tun bayan da ya kama aiki.

Sai dai kuma PRNigeria ta ruwaito cewa tuni a ka baiwa Fadah umarnin ya mika ragamar aiki ga ma’aikaci mafi matsayi a hukumar wanda zai zama shugaban na riƙo.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp