Home General Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga a Hare-Haren Sama da Suka Kaddamar Kan...

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga a Hare-Haren Sama da Suka Kaddamar Kan Maboyarsu a Kaduna da Zamfara

Rahotanni daga Najeriya na cewa sojoji sun kashe ‘yan bindiga da dama a hare-haren sama da suka kaddamar kan maɓoyarsu a jihohin Kaduna da Zamafara.

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta rawaito cewa a Kaduna, sojojin sun kai harin ne kan wani shugaban ‘yan bindiga Alhaji Gana a karamar hukumar Kinandan, da Ali Kawaje da Musa Pajelo da Kachalla Bello a Birnin Gwari.

An kuma tarwatsa ‘yan bindiga kuma a yankin Walawa da Fadaman Kanauta da Kuduru, kamar yada jaridar ta ambato Samuel Aruwan na cewa.

A Zamfara kuma jiragen sojin Najeriya sun yi luguden wuta a yankin Shinkafi. Kakakin sojojin Najeriya Edward Gabkwet ya ce jami’ansu na cigaba da daukar matakai fatatakar ‘yan bindiga a arewa maso yammacin Najeriya.

Hare-haren saman na zuwa ne kwanaki bayan ‘yan bindiga sun kashe mutum 44 a Zamfara.

Yankin arewacin Najeriya na fama da hare-haren ‘yan bindiga da satar mutane domin kudin fansa a shekarun baya-bayanan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp