Home SIYASA Cif Charles Udeogaranya ya Gargadi ‘Yan Nijeriya Kan Zaben Atiku ko Tinubu

Cif Charles Udeogaranya ya Gargadi ‘Yan Nijeriya Kan Zaben Atiku ko Tinubu

Cif Charles Udeogaranya, ya ja hankalin Al’ummar Nijeriya kan babban zaben kasar dake kara karatowa, inda yace kada su sake suyi uskerin yin zaben tumun dare a kakakar zaben 2023 mai karatowa

Udeogaranya wanda guda ne cikin tsuffin jiga-jigai a jam’iyya mai mulkin kasar ta APC  ya yiwa al’ummar kasar albishir da shan bakar wahala da shiga kangin talauci idan har suka ki zaban Peter Obi na jam’iyyar LP a matsayin shugaban kasa a zabe mai zuwa.

Tsohon jigon na APC ya shawarci ‘yan Najeriya da su kauracewa Bola Tinubu da Atiku Abubakar a 2023 idan har suna son kansu da arziki.

Cif Charles wanda tsohon dan takarar shugaban kasar ne a zaben 2019, ya shawarci ‘yan Najeriya game da wanda ya kamata su zaba a matsayin wanda zai gaji shugaban kasa Muhammadu Buhari a babban zabe mai zuwa.

Udeogaranya ya gargadi ‘yan Najeriya a kan su shirya shan bakar wahala da tabarbarewar tattalin arziki idan suka ki zaban dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi a 2023.

Gargadin tsohon jigon na jam’iyyar APC na zuwa ne sa’o’i 74 bayan hukumar kididdiga ta kasa ta bayyana cewa ‘yan Najeriya miliyan 133 ne fama da talauci, lamarin da ya dare hasashen bankin duniya kan Najeriya.

A wani jawabi da ya saki a Abuja a ranar Lahadi, dan siyasar ya gargadi yan Najeriya masu zabe wadanda basa daukar batun zaban ingantaccen shugaba muhimmanci da su zauna su sake tunani game da bakar wahala da talaucin mutuwa da zai dabaibayekasar.

Idan yan Najeriya sun san abun da ya fi masu to su kauracewa APC da PDP a 2023

Tsohon mai neman takarar shugaban kasar ya bukaci yan Najeriya da su kauracewa yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun All Progressives Congress (APC) da Peoples Democratic Party (PDP).

A cewarsa duk kanwar j ace kuma yakamata mutanen da suka wuce lokacinsu su ba da damar da Najeriya zata rayu idan har suna nufin kasar da alkhairi.

Dan siyasan ya kare kalaman sa  da cewa:

“Idan bamu wuce yan takarar shugaban kasa na APC da PDP ba, za su wuce da kaso 99.9 dinmu zuwa kangin talauci da bakar wahala.”

Muna bayan Peter Obi a 2023 don zagayen Inyamurai ne, Ohanaeze

Jaridar Punch ta rahoto cewa, a bangaren kungiyar Ohanaeze Ndigbo ta ayyana goyon bayanta ga takarar shugabancin Peter Obi a zaben 2023.

A cewar babban kungiyar mai kare muradan Inyamurai yanzu zagayen kudu maso gabas ne ya samar da shugaban kasar Najeriya na gaba.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp