Home DUNIYA Babu Gudu ba Ja Da Baya Kan Sabon Tsarin Takaita Cire Kudi...

Babu Gudu ba Ja Da Baya Kan Sabon Tsarin Takaita Cire Kudi – Godwin Emefiele

Babban bankin Najeriya, ya ce babu fashi kan sabon tsarinsa na takaitawa ɗaidaikun mutane cire kudi daga bankuna bayan kiraye-kiraye daga ko’ina a Najeriya cewar ya sake duba batun.

Gwamnan babban bankin, Godwin Emefiele ne ya bayyanawa manema labarai hakan a jiya Alhamis bayan ganawa da shugaba Muhammadu Buhari.

Ya ce batun da bankin zai sake dubawa shine adadin kudin da za a iya cirewa ba wai ya canja tsarin ba, inda ya ce sabon tsarin na nan daram.

Gwamnan babban bankin na magana ne bayan da majalisar wakilai ta nemi da a soke tsarin da kuma gayyatarsa zuwa gabanta domin ya yi mata bayani.

“Ina sane da batun jin karin bayani da ‘yan majalisa suka nema. Amma ina ganin abu mafi muhimmanci shi ne cewa tsarin ya faro ne tun a shekara ta 2012,” in ji Emefiele.

“Sai dai kusan sau uku zuwa hudu muna soke tsarin saboda muna ganin ya kamata mu yi kyakkyawan shiri da sake gyara tsarin biyan kudi a Najeriya.

”Tsakanin 2012 zuwa 2022, kusan shekara goma kenan, muna da yakinin cewa an samar da cibiyoyi na taimakawa mutane da dama yin hada-hadar kudaɗe a fadin kasa.

Emefiele ya ce akwai tsari da za a yi wa al’ummomi a karkara don tabbatar da cewa sabbin tsare-tsare ba su yi mummunan tasiri a kansu ba.

A ranar Talata ne, CBN ya taƙaita yawan kuɗade laƙadan da ƴan ƙasar za su iya cirewa daga asusun ajiyarsu na banki, inda yawan kuɗin da mutum ɗaya zai iya fitarwa a banki a sati shi ne naira 100,000 yayin da kamfani zai cire naira 500,000 ne kawai a sati.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp