Home General Dakarun Rundunar sojin saman Nijeriya sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan Ta’adda...

Dakarun Rundunar sojin saman Nijeriya sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan Ta’adda a Jihar Kaduna

Dakarun Rundunar sojin saman Nijeriya sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yar Ta’adda a kananan hukumomin Chikum da Igabi a jihar kaduna.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da al’amarun cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fitar.
Sanarwar tace a wani bangare na atisayen kawar da ‘yan ta’adda a fadin jihar, Dakarun sojin Nijeriya sun tabbatar da tarwatsa maboyar ‘yan ta’addan tare da tarwatsa ‘yan Ta’addan a wani sabon hari.
Haka kuma dakarun sun tarwatsa wata maboyar da makamin roket a maboyar su dake dajikan Kofita da Kuyanbana na karamar hukumar Birnin Gwari.

Da kuma wasu maboyar su a Kuduru da Gonan Baturiya dske nisan kilomita 4 yamma da Nabango.
A yayin da dakarun ke gudanar da atisaye a yankunan Karshi, Kerawa da Walawa a kananan Hukumomin of Igabi da Giwa inda aka hangi maboyar taso mai nisan kilomita 6 gudu maso yammacin Kerawa.
Gwamnatin jihar Kaduna ta karbu rahoton tare da yabawa dakarun sojin bisa namijin kokarin su na kawar da ‘yan ta’adda a jihar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp