Home DUNIYA Sojojin Nijeriya na cigaba da samun Nasarar kan mayan Boko Haram a...

Sojojin Nijeriya na cigaba da samun Nasarar kan mayan Boko Haram a Arewa maso gabashin Kasar

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami nasarar kama mayakan boko haram, tare da hallaka wasu a mafa
Rundunar sojojin nijeriya karkashin Dakarun operation hadin kai bisa hadin gwiwa da jami’an sa kai na vigilanti a daren litinin sun sami nasara hallaka mayakan boko haram 8 tare da kama guda a raye a wani harin kwanton bauna da suka gudanar a karamar hukumar Mafa dake jihar Borno a Arewa maso gabashin Nijeriya.
Wannan na zuwa ne bayan da hafsan hafsoshin Sojin Nijeriya Laftanal Janar Farouk Yahaya, ya bukaci dakarun sojin da su sake matsa kaimi wajen kai hare-hare ga ‘yan ta’addan dake cikin dajin Sambisa da kuma yankin tafkin Chadi.
Jaridar PRnigeria ta tattaro cewa dakarun sojin sun sami nasarar kai harin kwanton baunar ne bayan wasu bayanan sirri da suka samu a kauyen Ngoum dake kusa da garin Maiduguri babban birnin jihar ta Borno, hakan ya basu damar fatattakar mayakan.
‘yan ta’addan da dakarun suka hallaka sune wadanda ke aikata fashi da makami a dukkan fadin kananan hukumomin Mafa, jere da kunduga
Dakarun sun sami nasarar halaka 8 daga cikin su tare da kama guda 1 da raia, sai kuma nasarar kwato baburan hawa da kuma bindiga kirar AK47 a cewa PRNigeria.
Haka kuma a wani cigaban wata kungiya daga cikin Al’ummar kauyen kwayam a jihar borno sun sami nasarar halaka wasu ‘yan ta’adda da ake kyautata zaton mayan boko haram ne, a wani harin kwanton bauna da suka gudanar da makamin kwari da baka.
Majiyoyin sun kuma tabbatar da cewa matasan kauyen sun sami nasarar kwato babur din hawa guda daya inda suka mika shi ga hannun dakarun sojojin dake Gwongulan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp