Home DUNIYA Sojojin Nijeriya na cigaba da samun Nasarar kan mayan Boko Haram a...

Sojojin Nijeriya na cigaba da samun Nasarar kan mayan Boko Haram a Arewa maso gabashin Kasar

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami nasarar kama mayakan boko haram, tare da hallaka wasu a mafa
Rundunar sojojin nijeriya karkashin Dakarun operation hadin kai bisa hadin gwiwa da jami’an sa kai na vigilanti a daren litinin sun sami nasara hallaka mayakan boko haram 8 tare da kama guda a raye a wani harin kwanton bauna da suka gudanar a karamar hukumar Mafa dake jihar Borno a Arewa maso gabashin Nijeriya.
Wannan na zuwa ne bayan da hafsan hafsoshin Sojin Nijeriya Laftanal Janar Farouk Yahaya, ya bukaci dakarun sojin da su sake matsa kaimi wajen kai hare-hare ga ‘yan ta’addan dake cikin dajin Sambisa da kuma yankin tafkin Chadi.
Jaridar PRnigeria ta tattaro cewa dakarun sojin sun sami nasarar kai harin kwanton baunar ne bayan wasu bayanan sirri da suka samu a kauyen Ngoum dake kusa da garin Maiduguri babban birnin jihar ta Borno, hakan ya basu damar fatattakar mayakan.
‘yan ta’addan da dakarun suka hallaka sune wadanda ke aikata fashi da makami a dukkan fadin kananan hukumomin Mafa, jere da kunduga
Dakarun sun sami nasarar halaka 8 daga cikin su tare da kama guda 1 da raia, sai kuma nasarar kwato baburan hawa da kuma bindiga kirar AK47 a cewa PRNigeria.
Haka kuma a wani cigaban wata kungiya daga cikin Al’ummar kauyen kwayam a jihar borno sun sami nasarar halaka wasu ‘yan ta’adda da ake kyautata zaton mayan boko haram ne, a wani harin kwanton bauna da suka gudanar da makamin kwari da baka.
Majiyoyin sun kuma tabbatar da cewa matasan kauyen sun sami nasarar kwato babur din hawa guda daya inda suka mika shi ga hannun dakarun sojojin dake Gwongulan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp