Home DUNIYA Sojojin Nijeriya na cigaba da samun Nasarar kan mayan Boko Haram a...

Sojojin Nijeriya na cigaba da samun Nasarar kan mayan Boko Haram a Arewa maso gabashin Kasar

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami nasarar kama mayakan boko haram, tare da hallaka wasu a mafa
Rundunar sojojin nijeriya karkashin Dakarun operation hadin kai bisa hadin gwiwa da jami’an sa kai na vigilanti a daren litinin sun sami nasara hallaka mayakan boko haram 8 tare da kama guda a raye a wani harin kwanton bauna da suka gudanar a karamar hukumar Mafa dake jihar Borno a Arewa maso gabashin Nijeriya.
Wannan na zuwa ne bayan da hafsan hafsoshin Sojin Nijeriya Laftanal Janar Farouk Yahaya, ya bukaci dakarun sojin da su sake matsa kaimi wajen kai hare-hare ga ‘yan ta’addan dake cikin dajin Sambisa da kuma yankin tafkin Chadi.
Jaridar PRnigeria ta tattaro cewa dakarun sojin sun sami nasarar kai harin kwanton baunar ne bayan wasu bayanan sirri da suka samu a kauyen Ngoum dake kusa da garin Maiduguri babban birnin jihar ta Borno, hakan ya basu damar fatattakar mayakan.
‘yan ta’addan da dakarun suka hallaka sune wadanda ke aikata fashi da makami a dukkan fadin kananan hukumomin Mafa, jere da kunduga
Dakarun sun sami nasarar halaka 8 daga cikin su tare da kama guda 1 da raia, sai kuma nasarar kwato baburan hawa da kuma bindiga kirar AK47 a cewa PRNigeria.
Haka kuma a wani cigaban wata kungiya daga cikin Al’ummar kauyen kwayam a jihar borno sun sami nasarar halaka wasu ‘yan ta’adda da ake kyautata zaton mayan boko haram ne, a wani harin kwanton bauna da suka gudanar da makamin kwari da baka.
Majiyoyin sun kuma tabbatar da cewa matasan kauyen sun sami nasarar kwato babur din hawa guda daya inda suka mika shi ga hannun dakarun sojojin dake Gwongulan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp