Home General Majalisar dattawan Najeriya ta amince da ƙaramin kasafin kuɗi da shugaban ƙasar...

Majalisar dattawan Najeriya ta amince da ƙaramin kasafin kuɗi da shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya aike mata

Majalisar dattawan Najeriya ta amince da ƙaramin kasafin kuɗi da shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya aike mata na naira biliyan 819.5

Majalisar ta amince da kasafin ranar Laraba, bayan da ta yi nazari tare da amincewa da rahoton kwamitin majalisar kan kasafin kuɗi wanda Sanata Barau Jibrin ya jagoranta.

Sanata Barau ya ce za a yi amfani da kuɗin ne wajen kammala wasu manyan ayyukan, ciki har da gyaran hanyoyi da madatsun ruwan da ambaliya ta lalata.

Ya ƙara da cewa za a samu kuɗin ne daga basussuka na cikin gida da gwamnatin tarayya za ta ciyo.

A cikin wasiƙarsa ta aike wa majalisar dokoki kasar kasafin kuɗin, shugaba Buhari ya ce ”ƙasar ta fuskanci mummunar ambaliya a wannan shekarar, wacce ta haddasa cinye gonaki a yayin da ake dab da girbe amfanin gona. Hakan kuma ka iya kawo matsalar karancin abinci a ƙasar”.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp