Home General TCN zata ruguje gidaje dubu 1 a jihar kano

TCN zata ruguje gidaje dubu 1 a jihar kano

Kamfanin dakon wutar lantarki na Nijeriya (TCN) ya bayyana cewa babu gudu ba ja da baya kan yunkurin s ana ruguje gidaje dubu 1 da aka gin aba bisa ka’ida ba karkashi turakun wayoyin lanatarki a jihar kano.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da kamfanin ke musanta cewa gidajen da aka ware domin rugujewa sun haura dubu 20, inda kamfanin yace tun daga dan’agundi zuwa kumbotso gidaje da gine-gine da ba kamala ba basu wuce 100 ba.
Mataimakin Babban daraktan kamfanin, Alh. Muhammad Kamaru Bello, yace layin wayar wutar lantarki guda daya ne ya kawo wuta jihar kano daga jihar Kaduna wanda kuma aka hada shi tsahon shekaru 50 da suka gabata.
Sai dai mafi yawa daga cikin su an gaza biyan su hakkokin su, kuma hakn ya biyo bayan biyan daiyyar naira biliyan 1.5 yayin da kano ta biya naira miliyan 500 a tashar wutar ta Dan’Agundi da tashar rimin zakara.
Yace tashar wutar ta Dan’aAgundi an samar da ita ne shekaru hamsim da suka gabata, wadda take bada megawatts 80, amma zuwa yamzun tana samar da sama da megawatt 280 wannan ne ya sanya za’a gudanar da aikin.
Ya bayyana cewa dukkan wasu shirye-shirye wajen gudanar da aikin nan da kwanaki masu zuwa, za’a fara aikin sake gina layukan samar da wutar lantarki na biyu daga kano zuwa kaduna, yace babu gudu babu ja da baya.
PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp