Home General Kwalejin horas da jami’an ‘yan sanda ta Maiduguri ta yayi jami’ai 1180

Kwalejin horas da jami’an ‘yan sanda ta Maiduguri ta yayi jami’ai 1180

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya a ranar 29 ga watan Disamba 2022, ta yaye jumullar ‘yan sanda dubu daya da dari daya da tamanin (1180) daha kwalejin ‘yan sanda ta Maiduguri, dake jihar Borno a arewa maso gabashin Nijeriya, ‘yan sandan na cikin wadanda sukayi nasara daga cikin ‘yan sanda dubu goma na shekarar 2021 da suka je atisayen daukar aikin.
Wannan na kushe ta ciki wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ASP Sani Kamilu Shatambaya, a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar Borno; sanarwar tace an gudanar faretin bikin yayi ‘yan sandan a lokaci guda a kwalejojin ‘yan sanda da ke fadin kasar inda aka kamala atisaye na tsawon watannin shida.
A yayin taron yaye ‘yan sanda an gabatar da kyaututtuka ga ‘yan sandan da dama da suka gudanar da abin yabawa.
Da yake jawabi a yayin taron babban sifeton ‘yan sandan Nijeriya Usman alkali baba Psc(+) NPM, fdc NEAPS, CFR wanda ya sami wakilcin mataimakin babban sifeton ‘yan sandan mai lura da sashen ‘yan sanda kwantar da tarzoma AIG ALI JANGA, ya bukaci sabbin ‘yan sanda dasu kasance masu gaskiya da Da’a wannan zai taimaka musu wajen cimma gaci a lokacinda suke gudanar da ayyukan su.
Sifeton janar din ya kuma bayyana cewa, za’a mayar da kananan ‘yan sandan zuwa kananan hukumominsu na asali domin cigaba da sanya dabarun ‘yansan na gwamnatin tarayya na mangace aikata gama-garin laifuka, tare da dakile aikata manyan laifukan a wuraren da aka turasu.
Kwamandan kwalejin DCP Bethrand Onuoha, da yake jawabin rufe taro, ya godewa babban sefeton ‘yan sandan Nijeriya, sannan ya bukaci sabbin ‘yan sanda dasu yi amfani da abinda aka koyar da su.
Kwamishinonin ‘yan sandan jihar Borno, Yobe da kuma Adamawa da kuma wasu manyan jami’an ‘yan sandan Nijeriya sun sami halartar taron yaye jami’an.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp