Home General Buhari: Kamfanin samar da karafa na Ajaokuta zai ke samar da $1.6bn...

Buhari: Kamfanin samar da karafa na Ajaokuta zai ke samar da $1.6bn tare da sabbin masu zuba jari duk shekara.

Shugaban Nijeriya Muhammad Buhari yace kamfanin samar da karafa na Ajakuta zai ke samar da dala biliyan 1.6 dukkan shekara tare da samar da guraban ayyuka ga matasan kasar.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Mai Magana da yawun shugaban kasar Malam garba shehu ya fitar, wadda tace shugaban kasar ya bayyana hakan ne a fadar ohinoyi na garin Ebira, wanda kuma ya kaddamar da ziyarar aiki ta kwana guda a garin Okene na jihar kogi ranar Alhamis.
Shehu ya bayyana cewa Buhari ya magantu kan kudirin gwamnatin sa na mayar da jihar kogi matsayin cibiyar masana’antu kuma jihar da zata zama wajen samar da albakatun kasa.
Shugaban ya bayyana yadda gwamantin tarayya ta cimma matsaya kan dukkan wata doka da zata kawo tasgaro ga ciban kamfanin samar da karafan na Ajaokuta.
Inda yace aikin zai matukar amfanar da Al’ummar jihar
Shugaban y ace jihar kogi za kuma ta ci gajiyar aikin ta hanyoyi daban-daban musamman idan bututun iskar gas na AKK daya ratsa ta cikin jihar mai tsawon kilmita 614 (mil 384) wanda ake sa ran fara aikin sa a shekarar 2023.
Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar sa ta APC ta cika dukkan Alkawuran data daukarwa Al’ummar Nijeriya a ko wanne mataki.
Daga bisa ya bayyana cewa gwamnan jihar Yahaya Bello yayi abin a yaba a lokacin mulkinsa na tsahon shekaru 8 wato zango biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp