Home General Buhari: Kamfanin samar da karafa na Ajaokuta zai ke samar da $1.6bn...

Buhari: Kamfanin samar da karafa na Ajaokuta zai ke samar da $1.6bn tare da sabbin masu zuba jari duk shekara.

Shugaban Nijeriya Muhammad Buhari yace kamfanin samar da karafa na Ajakuta zai ke samar da dala biliyan 1.6 dukkan shekara tare da samar da guraban ayyuka ga matasan kasar.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Mai Magana da yawun shugaban kasar Malam garba shehu ya fitar, wadda tace shugaban kasar ya bayyana hakan ne a fadar ohinoyi na garin Ebira, wanda kuma ya kaddamar da ziyarar aiki ta kwana guda a garin Okene na jihar kogi ranar Alhamis.
Shehu ya bayyana cewa Buhari ya magantu kan kudirin gwamnatin sa na mayar da jihar kogi matsayin cibiyar masana’antu kuma jihar da zata zama wajen samar da albakatun kasa.
Shugaban ya bayyana yadda gwamantin tarayya ta cimma matsaya kan dukkan wata doka da zata kawo tasgaro ga ciban kamfanin samar da karafan na Ajaokuta.
Inda yace aikin zai matukar amfanar da Al’ummar jihar
Shugaban y ace jihar kogi za kuma ta ci gajiyar aikin ta hanyoyi daban-daban musamman idan bututun iskar gas na AKK daya ratsa ta cikin jihar mai tsawon kilmita 614 (mil 384) wanda ake sa ran fara aikin sa a shekarar 2023.
Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar sa ta APC ta cika dukkan Alkawuran data daukarwa Al’ummar Nijeriya a ko wanne mataki.
Daga bisa ya bayyana cewa gwamnan jihar Yahaya Bello yayi abin a yaba a lokacin mulkinsa na tsahon shekaru 8 wato zango biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp