Home General Buhari: Kamfanin samar da karafa na Ajaokuta zai ke samar da $1.6bn...

Buhari: Kamfanin samar da karafa na Ajaokuta zai ke samar da $1.6bn tare da sabbin masu zuba jari duk shekara.

Shugaban Nijeriya Muhammad Buhari yace kamfanin samar da karafa na Ajakuta zai ke samar da dala biliyan 1.6 dukkan shekara tare da samar da guraban ayyuka ga matasan kasar.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Mai Magana da yawun shugaban kasar Malam garba shehu ya fitar, wadda tace shugaban kasar ya bayyana hakan ne a fadar ohinoyi na garin Ebira, wanda kuma ya kaddamar da ziyarar aiki ta kwana guda a garin Okene na jihar kogi ranar Alhamis.
Shehu ya bayyana cewa Buhari ya magantu kan kudirin gwamnatin sa na mayar da jihar kogi matsayin cibiyar masana’antu kuma jihar da zata zama wajen samar da albakatun kasa.
Shugaban ya bayyana yadda gwamantin tarayya ta cimma matsaya kan dukkan wata doka da zata kawo tasgaro ga ciban kamfanin samar da karafan na Ajaokuta.
Inda yace aikin zai matukar amfanar da Al’ummar jihar
Shugaban y ace jihar kogi za kuma ta ci gajiyar aikin ta hanyoyi daban-daban musamman idan bututun iskar gas na AKK daya ratsa ta cikin jihar mai tsawon kilmita 614 (mil 384) wanda ake sa ran fara aikin sa a shekarar 2023.
Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar sa ta APC ta cika dukkan Alkawuran data daukarwa Al’ummar Nijeriya a ko wanne mataki.
Daga bisa ya bayyana cewa gwamnan jihar Yahaya Bello yayi abin a yaba a lokacin mulkinsa na tsahon shekaru 8 wato zango biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp