Home General Bincike: Shin gaskiya ne hukumar Kwallon kafa ta Duniya FIFA zata Ajje...

Bincike: Shin gaskiya ne hukumar Kwallon kafa ta Duniya FIFA zata Ajje Kafafun Pele a gidan Tarihi?

Wani labari na yawo a kafafen sada zumunta na zamani cewa hukunar FIFA zata ajje kafafun Pele a gidan tarihi.
Cikakken Labarin: Wallafar tace Yanzu Yanzu: “FIFA zata Ajje
Kafafun Pele a gidan Adana kayan Tarihi, kuma iyalensa Sun Amince.”
FIFA hukumar kwallon kafa ce da aka samar da ita a shekarar 1904.
Shi kuwa Pele wato, Edson Arantes do Nascimento, wanda aka fi sani da Pele dan kasar Brazil ne, kuma hamshakin dan wasa daya bawa kasar muhimmiyar gudunmawa ga tawagar kasar, wanda kuma ke da muhimmanci ga hukumar ta FIFA. Kuma guda cikin wadanda suka sami gagarumar nasara cikin ‘yan wasan karni na 20 a kasar sa.
Suna kiransa da Sarki, kuma fuskar sa na cikin fuskokin da aka fi ganewa a duniyar kwallon kafa. FIFA ta ambace shi da dan wasa mafi daraja a karni na 20.
Hamshakin dan wasan na tawagar Brazil ya mutu a ranar 29 ga watan Disambar 2022.
Tauraruwar Pele ta fara haskawa tun yana dan shekaru 17 a duniya, lokacin daya sami nasarar lashe gasar cin kofin duniya da aka gudabar a kasar Sweden a ranar 29 Yunin 1958.
Ya juma cigaba da rike kambunsa na mafi kankantar shekaru a duniya.
Gaskiyar Labarin: Bayan gudanar da bincike a kafar Intanet, ya bamu sami wani labari dake da alaka ta kusa ko ta nesa da wannan labarin ba daga kafar yada labarai sahihiya.
Haka kuma shafin da aka samar domin karbar gaisuwar mutuwar Pele ba sanar da wannan labarin ba.

Haka kuma mun bincika shafin hukumar ta FIFA musamman shafukan twitter, Instagram babu wata sanarwa makamanciyar wannan.
Sai dai wasu tashoshi a dandadin YouTube da twitter sun tabbatar da labarin tare da yada shi.
A Takaice: babu wata sanarwa daga hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA, dake cewa za’a Ajje Kafafun Pele a gidan tarihi kuma iyalen sa sun Amince.

Dan haka PRNigeria ta tabbatar da cewa labarin nan ba gaskiya bane ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp