Home General Bincike: Shin gaskiya ne hukumar Kwallon kafa ta Duniya FIFA zata Ajje...

Bincike: Shin gaskiya ne hukumar Kwallon kafa ta Duniya FIFA zata Ajje Kafafun Pele a gidan Tarihi?

Wani labari na yawo a kafafen sada zumunta na zamani cewa hukunar FIFA zata ajje kafafun Pele a gidan tarihi.
Cikakken Labarin: Wallafar tace Yanzu Yanzu: “FIFA zata Ajje
Kafafun Pele a gidan Adana kayan Tarihi, kuma iyalensa Sun Amince.”
FIFA hukumar kwallon kafa ce da aka samar da ita a shekarar 1904.
Shi kuwa Pele wato, Edson Arantes do Nascimento, wanda aka fi sani da Pele dan kasar Brazil ne, kuma hamshakin dan wasa daya bawa kasar muhimmiyar gudunmawa ga tawagar kasar, wanda kuma ke da muhimmanci ga hukumar ta FIFA. Kuma guda cikin wadanda suka sami gagarumar nasara cikin ‘yan wasan karni na 20 a kasar sa.
Suna kiransa da Sarki, kuma fuskar sa na cikin fuskokin da aka fi ganewa a duniyar kwallon kafa. FIFA ta ambace shi da dan wasa mafi daraja a karni na 20.
Hamshakin dan wasan na tawagar Brazil ya mutu a ranar 29 ga watan Disambar 2022.
Tauraruwar Pele ta fara haskawa tun yana dan shekaru 17 a duniya, lokacin daya sami nasarar lashe gasar cin kofin duniya da aka gudabar a kasar Sweden a ranar 29 Yunin 1958.
Ya juma cigaba da rike kambunsa na mafi kankantar shekaru a duniya.
Gaskiyar Labarin: Bayan gudanar da bincike a kafar Intanet, ya bamu sami wani labari dake da alaka ta kusa ko ta nesa da wannan labarin ba daga kafar yada labarai sahihiya.
Haka kuma shafin da aka samar domin karbar gaisuwar mutuwar Pele ba sanar da wannan labarin ba.

Haka kuma mun bincika shafin hukumar ta FIFA musamman shafukan twitter, Instagram babu wata sanarwa makamanciyar wannan.
Sai dai wasu tashoshi a dandadin YouTube da twitter sun tabbatar da labarin tare da yada shi.
A Takaice: babu wata sanarwa daga hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA, dake cewa za’a Ajje Kafafun Pele a gidan tarihi kuma iyalen sa sun Amince.

Dan haka PRNigeria ta tabbatar da cewa labarin nan ba gaskiya bane ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp