Home General Tunubu alkawarin bunkasa tsaro da harkokin tattalin arzikin jihar kano idan ya...

Tunubu alkawarin bunkasa tsaro da harkokin tattalin arzikin jihar kano idan ya sami nasara

Dan takarar shugabancin Nijeriya na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya yi alkawarin bunkasa tsaro da harkokin tattalin arzikin jihar kano idan ya sami nasara.

Tinubu ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da malaman Arewa maso yammacin Nigeria a jihar Kano.

Yace kasancewar kano cibiyar Arewacin Nigeria akwai bukatar a bata kulawa ta musamman saboda idan ta bunkasa dukkanin jihohin Arewacin Nigeria sun bunkasa.

Bola Tinubu ya kuma yi alkawarin samar da wani tsari da zai taimaka wajen inganta harkokin karatun al-qur’ani saboda magance matsalar barace-barace a kasar.

Ya kuma yi alkawarin baiwa malamai dama a gwamnatin tarayya ta yadda za’a dama da su domin inganta kasar. Tinubu ya bukaci Malamai da su umarci dalibansu da sauran magoya bayansu da su zabe shi saboda yafi dukkanin yan takarar shugaban kasa chanchanta.

Da yake nasa jawabin gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ƙalubalanci masu ganin baiken jam’iyyar APC don ta haɗa yan takarar shugaban kasa duk Musulmi, Inda yace haɗa Musulmi da Musulmi a takarar shugaban kasa ba sabon Abu bane a Ƙasar Nijeriyar .

Ganduje ya kuma bada tabbacin cewa al’ummar Nigeria suna son jam’iyyar APC da yan takarar su Kuma zasu zabe su a babban zaben Mai zuwa .

Malamai da dama ne dai suka halarci taron ganawar  wadanda suka fito daga jihohin Arewacin Nigeria domin halartar taron wanda ke cikin jerin tarukan da aka tsara don yakin neman zaben Tinubu a kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp