Home General Mai Martaba sarkin katsina ya nada shugaban hukumar NIA matsayin Sardaunan Katsina.

Mai Martaba sarkin katsina ya nada shugaban hukumar NIA matsayin Sardaunan Katsina.

Mai Martaba sarkin katsina ya nada shugaban hukumar NIA Ahmed Rufa’I matsayin Sardaunan katsina.
An nada babban daraktan hukumar tattara bayanan sirri Amb. Ahmed Rufa’I Abubakar matsayin sardaunan Katsina.
Mai martaba sarkin katsina Alhaji Abdulmumin Kabir Usman ya nada shugaban hukumar ta NIA matsayin sardaunan na katsina a ranar Asabar.
Taron nadin sarautar ya sami halartar manyan jami’an Gwamnatin Nijeriya, cikin su har da shugaban majalisar Dattawan Nijeriya, Ahmed Lawan.
Amb. Ahmed Rufa’I ya fito daga zuri’ar Muhammad Maude, Jarumi kuma sadauki, wanda tarihi ya nuna shine wanda ya samar da Unguwar Maude dake katsina a cikin a kashin farko cikin ukun karni na 19.
An gudanar da nadin ne a fadar mai martaba sarkin katsina, cikin nutsuwa da annashuwa, taron ya sami halartar manyan baki daga ciki da wajen kasar.
Da yake jawabi ga dimin jama’a da suka sami halartar taron nadin mai martaba sarkin Katsina, yace nadin sarautar sardaunar da aka yiwa shugaban hukumar ta NIA, ya nuna godiya da irin kyakkyawar hidimar da ya yiwa katsina, nijeriya da kuma tsarin kasa da kasa, gami da jajircewa wajen aiki tukuru da rikon amana.
Sarkin yayi kira ga sauran masu rike da madafun iko a Nijeriya da su yi aiki da aminci tare da sauke nauyin dake kan su.
Sarkin ya bayyana kabilanci da nuna banbancin addinin matsayin abinda ke kawo tasgaro ga hadin kan kasa, inda ya bukaci ‘yan kasar dasu kawar da su domin samun cigaban kasar.
Sabon sardaunan katsina, Ahmad Rufa’I Abubakaya sami lambobin yabo da dama. Suka hadar da DGNIA bisa kwazo sai kuma lambar yabo ta l’Ordre National de la Republique du Niger wanda shugaban jamhuriyyar Nijar ya damka masa, sai kuma lambar yabo ta CFR, wadda shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bashi, da dai sauran manyan lambobin girmamawa daya samu

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp