Home General Buhari ya gargadi masu shirin kawo cikas a zaben 2023

Buhari ya gargadi masu shirin kawo cikas a zaben 2023

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya yi gargadi wadanda ke kokarin kawo cikas ga zabukan da ake shirin gudanarwa cikin shekara ta 2023 a kasar cewa lalle za su hadu da fushin doka.
Shugaba Buhari ya yi wannan gargadi ne a jawabin da ya gabatar wa al’ummar kasar dangane da shiga sabuwar shekara ta 2023, yana mai kira ga illahirin ‘yan Najeriya da su tabbatar da wadannan zabuka sun gudana a cikin yanayi na tsari, ‘yanci da kuma mutunta doka.
Buhari ya ce watannin da ke gaba na da matukar muhimmanci ga gwamnatinsa, musamman a fannoni guda uku da suka hadar da tsaro, tattalin arziki da kuma ci gaba da yaki da rashawa a duk fadin kasar.
A wani bangare na jawabinsa, Muhammadu Buhari ya ce ya zama wajibi ga ‘yan Najeriya su tabbatar da cewa ‘yan siyasa ba su yi amfani da su domin tayar da fitina a lokacin wadannan zabuka da take ba.
Shugaban ya bayyana wasu daga cikin nasarorin da ya ce ya samu a cikin shekaru 7 da suka gabata, sannan ya ce yana murna ga wadanda ke yaba wa kokarin da ya yi da ma wadanda ke sukar salon mulkinsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp