Home General Buhari ya gargadi masu shirin kawo cikas a zaben 2023

Buhari ya gargadi masu shirin kawo cikas a zaben 2023

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya yi gargadi wadanda ke kokarin kawo cikas ga zabukan da ake shirin gudanarwa cikin shekara ta 2023 a kasar cewa lalle za su hadu da fushin doka.
Shugaba Buhari ya yi wannan gargadi ne a jawabin da ya gabatar wa al’ummar kasar dangane da shiga sabuwar shekara ta 2023, yana mai kira ga illahirin ‘yan Najeriya da su tabbatar da wadannan zabuka sun gudana a cikin yanayi na tsari, ‘yanci da kuma mutunta doka.
Buhari ya ce watannin da ke gaba na da matukar muhimmanci ga gwamnatinsa, musamman a fannoni guda uku da suka hadar da tsaro, tattalin arziki da kuma ci gaba da yaki da rashawa a duk fadin kasar.
A wani bangare na jawabinsa, Muhammadu Buhari ya ce ya zama wajibi ga ‘yan Najeriya su tabbatar da cewa ‘yan siyasa ba su yi amfani da su domin tayar da fitina a lokacin wadannan zabuka da take ba.
Shugaban ya bayyana wasu daga cikin nasarorin da ya ce ya samu a cikin shekaru 7 da suka gabata, sannan ya ce yana murna ga wadanda ke yaba wa kokarin da ya yi da ma wadanda ke sukar salon mulkinsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp