Home General Hukumar DSS zata Tabbatar da tsaftataccen Zabe a 2023 – Afunanya

Hukumar DSS zata Tabbatar da tsaftataccen Zabe a 2023 – Afunanya

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta tabbatarwa da Al’ummar kasar
dana duniya baki daya tsayawa tsayin daka wajen ganin an gudanar databbatar da sahihin zabe a shekarar 2023.

Hukumar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da kakakin ta
Hukumar ta DSS Peter Afunanya, ya fitar, yayin da yake musanta rade-radin da ake yi na cewa hukumar tana gaban kotu tare da shugaban hukumar zabe mai zaman kanta Mahmood Yakubu kan zargin kin bayyana kadarorin.

“Sanarwar tace, Hankalin hukumar ta DSS ya kai kan wallafar da wata jaridar yanar gizo tayi a ranar 5 ga watan
The statement said, “The attention of the Janairun 2023, wadda tace kuto ta dakatar da hukumar a kokarinta na kama shugaban hukumar zabe ta Kasar INEC.
“Hukumar ta gano cewa jaridar ta sauya ainihin abin da ya faru a kotun kuma ta ba da rahoton da bana gaskiya ba. Dangane da haka ne hukumar ta nuna rashin jin dadinta bisa abinda hukumar gudanarwar kamfanin jaridar ya aikata. Abinda jaridar ta wallafa yasha bamban da kwafin shari’ar, ta kuma yi alkawarin gyarawa amma bata gyara ba.

“Wannan magana, duk da haka, ta zama mai mahimmanci domin fahimtar jama’a don fahimtar juna, musamman ma saboda rahoton karya da aka yada. Na cewa shugaban hukumar ya garzaya kotu.

“Duk da haka, hukumar tana sane da yadda wasu bata-gari ke son tada rikici a kasar, gami da haifar da cece-kuce game da babban zabe mai zuwa.
“Na daga cikin dabarunsu shine kawo cikas ga kokarin tabbatar da zaman lafiya da lumana.

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a ranar Laraba ta yi watsi da zarge-zargen bayyana kadarorin karya da ake yi wa Yakubu tare da hana jami’an tsaro gudanar da bincike a kansa.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp