Home General Hukumar DSS zata Tabbatar da tsaftataccen Zabe a 2023 – Afunanya

Hukumar DSS zata Tabbatar da tsaftataccen Zabe a 2023 – Afunanya

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta tabbatarwa da Al’ummar kasar
dana duniya baki daya tsayawa tsayin daka wajen ganin an gudanar databbatar da sahihin zabe a shekarar 2023.

Hukumar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da kakakin ta
Hukumar ta DSS Peter Afunanya, ya fitar, yayin da yake musanta rade-radin da ake yi na cewa hukumar tana gaban kotu tare da shugaban hukumar zabe mai zaman kanta Mahmood Yakubu kan zargin kin bayyana kadarorin.

“Sanarwar tace, Hankalin hukumar ta DSS ya kai kan wallafar da wata jaridar yanar gizo tayi a ranar 5 ga watan
The statement said, “The attention of the Janairun 2023, wadda tace kuto ta dakatar da hukumar a kokarinta na kama shugaban hukumar zabe ta Kasar INEC.
“Hukumar ta gano cewa jaridar ta sauya ainihin abin da ya faru a kotun kuma ta ba da rahoton da bana gaskiya ba. Dangane da haka ne hukumar ta nuna rashin jin dadinta bisa abinda hukumar gudanarwar kamfanin jaridar ya aikata. Abinda jaridar ta wallafa yasha bamban da kwafin shari’ar, ta kuma yi alkawarin gyarawa amma bata gyara ba.

“Wannan magana, duk da haka, ta zama mai mahimmanci domin fahimtar jama’a don fahimtar juna, musamman ma saboda rahoton karya da aka yada. Na cewa shugaban hukumar ya garzaya kotu.

“Duk da haka, hukumar tana sane da yadda wasu bata-gari ke son tada rikici a kasar, gami da haifar da cece-kuce game da babban zabe mai zuwa.
“Na daga cikin dabarunsu shine kawo cikas ga kokarin tabbatar da zaman lafiya da lumana.

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a ranar Laraba ta yi watsi da zarge-zargen bayyana kadarorin karya da ake yi wa Yakubu tare da hana jami’an tsaro gudanar da bincike a kansa.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp