Home General Hukumar DSS zata Tabbatar da tsaftataccen Zabe a 2023 – Afunanya

Hukumar DSS zata Tabbatar da tsaftataccen Zabe a 2023 – Afunanya

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta tabbatarwa da Al’ummar kasar
dana duniya baki daya tsayawa tsayin daka wajen ganin an gudanar databbatar da sahihin zabe a shekarar 2023.

Hukumar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da kakakin ta
Hukumar ta DSS Peter Afunanya, ya fitar, yayin da yake musanta rade-radin da ake yi na cewa hukumar tana gaban kotu tare da shugaban hukumar zabe mai zaman kanta Mahmood Yakubu kan zargin kin bayyana kadarorin.

“Sanarwar tace, Hankalin hukumar ta DSS ya kai kan wallafar da wata jaridar yanar gizo tayi a ranar 5 ga watan
The statement said, “The attention of the Janairun 2023, wadda tace kuto ta dakatar da hukumar a kokarinta na kama shugaban hukumar zabe ta Kasar INEC.
“Hukumar ta gano cewa jaridar ta sauya ainihin abin da ya faru a kotun kuma ta ba da rahoton da bana gaskiya ba. Dangane da haka ne hukumar ta nuna rashin jin dadinta bisa abinda hukumar gudanarwar kamfanin jaridar ya aikata. Abinda jaridar ta wallafa yasha bamban da kwafin shari’ar, ta kuma yi alkawarin gyarawa amma bata gyara ba.

“Wannan magana, duk da haka, ta zama mai mahimmanci domin fahimtar jama’a don fahimtar juna, musamman ma saboda rahoton karya da aka yada. Na cewa shugaban hukumar ya garzaya kotu.

“Duk da haka, hukumar tana sane da yadda wasu bata-gari ke son tada rikici a kasar, gami da haifar da cece-kuce game da babban zabe mai zuwa.
“Na daga cikin dabarunsu shine kawo cikas ga kokarin tabbatar da zaman lafiya da lumana.

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a ranar Laraba ta yi watsi da zarge-zargen bayyana kadarorin karya da ake yi wa Yakubu tare da hana jami’an tsaro gudanar da bincike a kansa.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp