Home General Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sami Nasarar kama ‘yan daban Siyasa...

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sami Nasarar kama ‘yan daban Siyasa 61 dauke da makamai a jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta sami Nasarar kama ‘yan daban Siyasa 61 dauke da makamai a jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sami nasarar kama ‘yan daba 61 dauke da makamai da ake zargi da tada hargitsi, a kokarin rundunar dajike dukkan ayyukan Ta’addanci lokaxin yakin neman zabe.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Mamman Dauda, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna-Kiyawa, ya raba manema labarai a Kano.

Yace kame ya biyo baya umarnin babban sifeton
Janar na ‘yan sanda Nijeriya Usman Alkali-Baba, domin tabbatar da gudanar da ingantaccen zabe gami da dakile ayyukan daba a yayin zabe.
“wadanda ake zargin an kamasu ne a ranar 4 ga watan Janairu, yayin wani atasaye kakkabe barna a lokacin yakin neman zabe a filin wasa na Sani Abacha.

Yace an kwato makamai a hannun wadanda ake zargin da suka hadar da wukake 33, adduna 8, almakashi 4 sai kuma kunshin tabar wiwi guda 117.
Kwamishinan ya kara da cewa, kafin a fara gudanar da aikin, an gudanar da taron kwamitin tuntuba tsakanin hukumomin tsaro kan harkokin zabe da kuma taron zaman lafiya da ya kunshi dukkan masu ruwa da tsaki.
“An kuma gudanar da tarurruka da masu ruwa da tsaki akan zabe a kananan hukumomi, da kuma ofishoshin ‘yan Sanda.
“Shugabannin jam’iyyar siyasa da ‘yan takarkaru sun yi alkawarin bawa ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a jihar domin samun ingantaccen zabe mai inganci,” in ji shi.
Dauda ya yabawa al’ummar jihar da sauran hukumomin tsaro da kafafen yada labarai da kungiyoyin ‘yan masu zaman kansu da masu ruwa da tsaki a harkar ‘yan sanda bisa addu’o’i da goyon baya da karfafa gwiwa da hadin kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp