Home General Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sami Nasarar kama ‘yan daban Siyasa...

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sami Nasarar kama ‘yan daban Siyasa 61 dauke da makamai a jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta sami Nasarar kama ‘yan daban Siyasa 61 dauke da makamai a jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta sami nasarar kama ‘yan daba 61 dauke da makamai da ake zargi da tada hargitsi, a kokarin rundunar dajike dukkan ayyukan Ta’addanci lokaxin yakin neman zabe.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Mamman Dauda, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna-Kiyawa, ya raba manema labarai a Kano.

Yace kame ya biyo baya umarnin babban sifeton
Janar na ‘yan sanda Nijeriya Usman Alkali-Baba, domin tabbatar da gudanar da ingantaccen zabe gami da dakile ayyukan daba a yayin zabe.
“wadanda ake zargin an kamasu ne a ranar 4 ga watan Janairu, yayin wani atasaye kakkabe barna a lokacin yakin neman zabe a filin wasa na Sani Abacha.

Yace an kwato makamai a hannun wadanda ake zargin da suka hadar da wukake 33, adduna 8, almakashi 4 sai kuma kunshin tabar wiwi guda 117.
Kwamishinan ya kara da cewa, kafin a fara gudanar da aikin, an gudanar da taron kwamitin tuntuba tsakanin hukumomin tsaro kan harkokin zabe da kuma taron zaman lafiya da ya kunshi dukkan masu ruwa da tsaki.
“An kuma gudanar da tarurruka da masu ruwa da tsaki akan zabe a kananan hukumomi, da kuma ofishoshin ‘yan Sanda.
“Shugabannin jam’iyyar siyasa da ‘yan takarkaru sun yi alkawarin bawa ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro hadin kai a jihar domin samun ingantaccen zabe mai inganci,” in ji shi.
Dauda ya yabawa al’ummar jihar da sauran hukumomin tsaro da kafafen yada labarai da kungiyoyin ‘yan masu zaman kansu da masu ruwa da tsaki a harkar ‘yan sanda bisa addu’o’i da goyon baya da karfafa gwiwa da hadin kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp