Home General Wani harin mayakan Boko Haram ya yi Sanadiyyar Mayakan ISWAP.

Wani harin mayakan Boko Haram ya yi Sanadiyyar Mayakan ISWAP.

‘Yan Ta’addan kungiyar Boko haram sun fatattaki Mayakan iswap tare da hallaka 35 daga cikin su.

Hare-haren da bangarorin ke ci gaba da kai wa a sansanonin juna wanda kwamandan Boko Haram, ABU UMAIMAH ko BAKOURA DORO ne suka jagoranci kai harin tare da Kwamandoji hudu da wasu mayaka da dama.

Harin da aka fara a Arewacin Kayowa da Toumbun Gini, a Arewa maso Gabashin tafkin Chadi, ya kai ga halaka mayakan ISWAP 35 yayin da wasu da dama suka jikkata.

Zagazola ya rawaito cewa, kwamandan kungiyar Boko Haram maras tausayi ya kuma kwace makamai masu tarin yawa daga hannun ‘yan ta’addar ISWAP, yayin da suka tsere daga sansanonin su.

Majiyar ta bayyana cewa wata babbar kasuwa ta ISWAP dake Toumbun Gini, yan kungiyar JAS ne suka karbe ta a halin yanzu.

Zagazola ya fahimci cewa ‘yan ta’addan da suka tsere abikan gabar tasu sun bi su ne ta kudancin Kangarwa da Dogon Chuku a karamar hukumar Baga.

A makonnin da suka gabata, Yan ta’addan na Boko Haram, sun yi mummunar barna a sansanonin ISWAP da ke dajin Sambisa da kuma yankin tafkin Chadi, lamarin da ya tilastawa ISWAP daukar matakan kariya.

Ko da a ranar 31 ga watan Disamba, an kai hare-hare tsakanin bangarorin ISWAP da JAS da suka dauki tsawon sa’o’i 14 a yankunan Toumbum Allura da Kangar, inda aka kashe mayakan da dama.

Ya bayyana cewa ci gaba da kai hare-hare ya tilastawa mayakan na ISWAP gudanar da taro a Tumbun Murhu tare da manyan shugabannin ISWAP da suka hada da Abubakar Chad, Bashir Ukasha da Abul Kaka- Alias ​​Sa’ad.

Majiyar ta bayyana cewa, manyan batutuwan da aka tattauna a yayin taron su hadar da yadda kungiyarsu ta kasa kai wasu manyan hare-hare a lokacin bukuwan kirsimeti da sabuwar shekara kamar yadda aka tsara tun farko wanda ake dangantawa da fada da hare-haren da mayakan Boko Haram suka kai kan sansanonin ta.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp