Home General Ana cigaba da zaman makokin Jami’an Tsaron da ‘Yan Bindiga suka Hallaka...

Ana cigaba da zaman makokin Jami’an Tsaron da ‘Yan Bindiga suka Hallaka a jihar kaduna

A wani hari da ‘yan bindiga suka kai yankuna biyu na karamar hukumar Birnin Gwari na jihar Kaduna, ‘yan bindiga sun halaka jami’an tsaro da dama a yankin.

Rikicin ya samo asali ne, bayan jami’an tsaro sun kashe wani yaro makwanni uku da suka gabata, wanda yake kulawa ‘yan bindigan shanunsu.

Wannan ne ya sa ‘yan bindigar daukar fansa a ranar Litinin kan yankunan da mummunan lamarin ya auku na Kubau da Anguwan Zakara

‘Yan bindiga sun salwantar da rayukan jami’an tsaro da dama a yankuna biyu da inda suke cin karensu babu babbaka na karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, kamar yadda.

Daga cikin jami’an tsaron da suka rayukansu sun hada da; jami’an NSCDC, ‘yan sanda, soji da kuma wasu ‘yan sa kai a ranar Lahadi, kamar yadda majiyar ta bayyana.

“Ba ranar Lahadi bane suka fara harin, sai dai sun fara ne kwanaki hudu da suka wuce. An kai hari titin Funtua zuwa Birnin Gwari, inda jami’an tsaro da dama suka rasa rayukansu. Amma na ranar Lahadi, ‘yan sa kai biyu, ‘dan sanda daya da wani soja sun rasa rayukansu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp