Home General Ana cigaba da zaman makokin Jami’an Tsaron da ‘Yan Bindiga suka Hallaka...

Ana cigaba da zaman makokin Jami’an Tsaron da ‘Yan Bindiga suka Hallaka a jihar kaduna

A wani hari da ‘yan bindiga suka kai yankuna biyu na karamar hukumar Birnin Gwari na jihar Kaduna, ‘yan bindiga sun halaka jami’an tsaro da dama a yankin.

Rikicin ya samo asali ne, bayan jami’an tsaro sun kashe wani yaro makwanni uku da suka gabata, wanda yake kulawa ‘yan bindigan shanunsu.

Wannan ne ya sa ‘yan bindigar daukar fansa a ranar Litinin kan yankunan da mummunan lamarin ya auku na Kubau da Anguwan Zakara

‘Yan bindiga sun salwantar da rayukan jami’an tsaro da dama a yankuna biyu da inda suke cin karensu babu babbaka na karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, kamar yadda.

Daga cikin jami’an tsaron da suka rayukansu sun hada da; jami’an NSCDC, ‘yan sanda, soji da kuma wasu ‘yan sa kai a ranar Lahadi, kamar yadda majiyar ta bayyana.

“Ba ranar Lahadi bane suka fara harin, sai dai sun fara ne kwanaki hudu da suka wuce. An kai hari titin Funtua zuwa Birnin Gwari, inda jami’an tsaro da dama suka rasa rayukansu. Amma na ranar Lahadi, ‘yan sa kai biyu, ‘dan sanda daya da wani soja sun rasa rayukansu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp