Home General NNPC Tana Tafka Asara Wajen Sayar da Mai Saboda Umarnin Gwamnatin Tarayya...

NNPC Tana Tafka Asara Wajen Sayar da Mai Saboda Umarnin Gwamnatin Tarayya Kan Batun Tallafi – Timipre Sylva

Karamin Ministan Fetur a Najeriya ya ce NNPC tana tafka asara wajen sayar da mai saboda umarnin gwamnatin Tarayya kan batun tallafi.

Timipre Sylva ya shaida hakan ne adaidai lokacin da dillalan man fetur ke cewa suna fuskantar karanci mai lamarin da ka iya sake ta’azzara wahalar man har zuwa watan Yuni, saboda shirin gwamnati na janye tallafi baki ɗaya a wannan watan.

An rawaito ministan na waɗannan kalamai ne a yayin da yake bayyana abubuwan da suka aiwatar tsakanin 2015 zuwa 2023 karkashin mulkin Muhammadu Buhari.

A makon da ya gabata, Ministar kuɗi da tsare-tsare, Zainab Ahmed ta ce gwamnati ta ware naira tiriliyan 3.6 na tallafi fetur zuwa Yunin 2023.

An rawaito Sylva a lokacin zantawa da ‘yan jarida a Abuja, na cewa tallafin babban nauyi ne, sai dai kuma wajibi ne ga NNPC da aka daurawa alhakin tafiyar da harkokin fetur a kasar ta ci gaba da daukar asara.

Gwamnatin Najeriya a ranar Litinin ta bayyana cewa ta zuba hannayen jari a matatun mai hudu da ke shirin soma ayyukansu a sassa daban-daban a faɗin Kasar.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp