Home General NAHCON ta kula yarjejeniya da Saudiya akan yadda aikin hajji 2023 zai...

NAHCON ta kula yarjejeniya da Saudiya akan yadda aikin hajji 2023 zai kasance

Shugaban hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON Zikrullah Kulle Hassan ya jagoranci tawagar masu ruwa da tsaki zuwa kasa mai tsarki domin kulla yarjejeniya da hukumomi daban-daban na kasar Saudiya a wani mataki na fara shirye-shiryen aikin hajjin bana.

Bayanin hakan na kunshe cikin wata sanarwa da hukumar NAHCON ta fitar mai dauke da sa hanun mataimakin daraktar yada labanta Musa Uban Dawaki, inda yace manufar ziyar ita tattaunawa da masu ruwa da tsaki akan harkokin aikin Hajji dake kasar tare da kula yarjejeniya akan yadda aikin hajji 2023. zai guduna .

Rahotonni sun bayyana cewar tuni dai karamin ministan harkokin kasashen wajen Najeriya Ambasada Zubairu Dada ya sanya hannu a kan takaddar yarjejeniyar da aka cimma a kasa mai tsarki a madadin Najeriya.

A zantawarsa da manema labarai daga kasa maitarki kwamishinan hukumar mai kula da harkokin kudi da ma’aikata, Alhaji Nura Hassan Yakasai, ya ce hakan yana nufin kokarin da hukumar ke yi a karkashin jagorancin shugabanta Zikrullah Kulle Hassan na tabbatar da cewar aikin Hajjin 2023 ya zarta wadanda ake gudanarwa a baya cikin ikon Allah.
Sannan ya yi karin haske akan manufofin kulla yarjejeniyar da muhimmancin ta ga Najeriya.

Nura Hassan Yakasai, ya ce cikin ikon Allah shirin da NAHCON ke yi a wannan shekara ta nuna za’a samu nasara fiye da yadda ake gabatar shirin gudanar da aikin hajjin a shekaru baya.

Cikin tawagar akwai Karamin Ministan harkokin Kasashen waje na Najeriya Ambasada Zubairu Dada, da shugaban kwamitin harkokin kasashen waje a majalisar dattawa Sanata Adamu Bulkacuwa, sai shugaban kwamitin aikin hajji a majalisar wakilai ta tarayya Abubakar Hassan Na Laraba, kwamishinonin hukumar aikin hajjin gami da yan kwamitin gudanarwata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp