Home General NAHCON ta kula yarjejeniya da Saudiya akan yadda aikin hajji 2023 zai...

NAHCON ta kula yarjejeniya da Saudiya akan yadda aikin hajji 2023 zai kasance

Shugaban hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON Zikrullah Kulle Hassan ya jagoranci tawagar masu ruwa da tsaki zuwa kasa mai tsarki domin kulla yarjejeniya da hukumomi daban-daban na kasar Saudiya a wani mataki na fara shirye-shiryen aikin hajjin bana.

Bayanin hakan na kunshe cikin wata sanarwa da hukumar NAHCON ta fitar mai dauke da sa hanun mataimakin daraktar yada labanta Musa Uban Dawaki, inda yace manufar ziyar ita tattaunawa da masu ruwa da tsaki akan harkokin aikin Hajji dake kasar tare da kula yarjejeniya akan yadda aikin hajji 2023. zai guduna .

Rahotonni sun bayyana cewar tuni dai karamin ministan harkokin kasashen wajen Najeriya Ambasada Zubairu Dada ya sanya hannu a kan takaddar yarjejeniyar da aka cimma a kasa mai tsarki a madadin Najeriya.

A zantawarsa da manema labarai daga kasa maitarki kwamishinan hukumar mai kula da harkokin kudi da ma’aikata, Alhaji Nura Hassan Yakasai, ya ce hakan yana nufin kokarin da hukumar ke yi a karkashin jagorancin shugabanta Zikrullah Kulle Hassan na tabbatar da cewar aikin Hajjin 2023 ya zarta wadanda ake gudanarwa a baya cikin ikon Allah.
Sannan ya yi karin haske akan manufofin kulla yarjejeniyar da muhimmancin ta ga Najeriya.

Nura Hassan Yakasai, ya ce cikin ikon Allah shirin da NAHCON ke yi a wannan shekara ta nuna za’a samu nasara fiye da yadda ake gabatar shirin gudanar da aikin hajjin a shekaru baya.

Cikin tawagar akwai Karamin Ministan harkokin Kasashen waje na Najeriya Ambasada Zubairu Dada, da shugaban kwamitin harkokin kasashen waje a majalisar dattawa Sanata Adamu Bulkacuwa, sai shugaban kwamitin aikin hajji a majalisar wakilai ta tarayya Abubakar Hassan Na Laraba, kwamishinonin hukumar aikin hajjin gami da yan kwamitin gudanarwata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp