Hukumar zaɓe a Najeriya (INEC) ta tsawaita wa’adin karɓar katin zaɓe da take raba wa a faɗin ƙasar.

Shugaban Sashen Yaɗa Labarai na INEC, Festus Okoye ya ce an ɗauki matakin ne don bai wa masu kada kuri’a isasshen lokaci na karɓar katin kafin fara jefa ƙuri’a a babban zaɓe na 2023.

“Saboda wannan dalilin, an tsawaita wa’adin karɓar katin zaɓen da kwana takwas,” in ji shi.

“A maimakon 22nd ga watan Janairu, za a ci gaba da karɓa har zuwa Lahadi, 29 ga watan na Janairu.”

INEC ta ce lokacin karɓar katin shi ne 9:00 na safe zuwa 3:00 na yamma a kullum da ga Asabar zuwa Lahadi.

Kazalika, tsawaitawar ta shafi dukkan cibiyoyin karɓar katin a matakin ƙananan hukumomi da mazaɓu .

A ranar 25 ga watan Fabarairu ne za a fara kaɗa ƙuri’a, inda ake sa ran yan kasa miliyan 93.4 million da su ka yi rijistar zaɓe za su zaɓi shugaban ƙasa da ‘yan majalisar tarayya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp