Home General An bankado manyan kabari dake dauke gawar mutane 49 a Kasar Congo...

An bankado manyan kabari dake dauke gawar mutane 49 a Kasar Congo MDD.

Majalisar dinkin duniya ta bayyana cewa an sami wani babban kabari dake dauke da mutane 49 a Arewa maso gabashin kasar Kwango.
Mataimakin kakakin majalisar Farhan Haq ne ya bayyana hakan ga manema labarai a birnin New na kasar Amurka, inda yace an sami kaburran ne a wasu kauyuka 2 a yankin Ituri dake da nisan kilo miter 30 da birnin Bunia.
An sami adadin mutane 42 da suka hadar da yara 6 a wani babban kabari a kauyen Nyamamba, haka kuma an ga wasu gawarwaki maza 7 a kauyen Mbogi, a cewar Haq.
Hukumomin yankin sun bayyana cewa kungiyar ‘yan bindiga ta CODECO sun kuma yi awon gaba da wasu mata a hare-haren da aka kai kauyukan.
Ko dai a watan Yulin daya gabata, kungiyar ta CODECO su 7 suka sanar da kawo karshen cin zarafin fararen hula a garin Ituri, musamman Djugu inda suke da karfi. Amma duk da haka suka cigaba da kai hare-hare a yankin.
Akalla mutane 195 ne aka hallaka tun watan disamba a jirin hare-haren da ake zargin kungiyar CODECO da wasu kungiyoyi mas dauke da makamai a cewar MDD. Haka kuma fiye da mutane miliyan 1.5 suka rasa matsugunnin su a lardin Ituri biyo bayan hare-haren.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp