Home General An bankado manyan kabari dake dauke gawar mutane 49 a Kasar Congo...

An bankado manyan kabari dake dauke gawar mutane 49 a Kasar Congo MDD.

Majalisar dinkin duniya ta bayyana cewa an sami wani babban kabari dake dauke da mutane 49 a Arewa maso gabashin kasar Kwango.
Mataimakin kakakin majalisar Farhan Haq ne ya bayyana hakan ga manema labarai a birnin New na kasar Amurka, inda yace an sami kaburran ne a wasu kauyuka 2 a yankin Ituri dake da nisan kilo miter 30 da birnin Bunia.
An sami adadin mutane 42 da suka hadar da yara 6 a wani babban kabari a kauyen Nyamamba, haka kuma an ga wasu gawarwaki maza 7 a kauyen Mbogi, a cewar Haq.
Hukumomin yankin sun bayyana cewa kungiyar ‘yan bindiga ta CODECO sun kuma yi awon gaba da wasu mata a hare-haren da aka kai kauyukan.
Ko dai a watan Yulin daya gabata, kungiyar ta CODECO su 7 suka sanar da kawo karshen cin zarafin fararen hula a garin Ituri, musamman Djugu inda suke da karfi. Amma duk da haka suka cigaba da kai hare-hare a yankin.
Akalla mutane 195 ne aka hallaka tun watan disamba a jirin hare-haren da ake zargin kungiyar CODECO da wasu kungiyoyi mas dauke da makamai a cewar MDD. Haka kuma fiye da mutane miliyan 1.5 suka rasa matsugunnin su a lardin Ituri biyo bayan hare-haren.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp