Home General An bankado manyan kabari dake dauke gawar mutane 49 a Kasar Congo...

An bankado manyan kabari dake dauke gawar mutane 49 a Kasar Congo MDD.

Majalisar dinkin duniya ta bayyana cewa an sami wani babban kabari dake dauke da mutane 49 a Arewa maso gabashin kasar Kwango.
Mataimakin kakakin majalisar Farhan Haq ne ya bayyana hakan ga manema labarai a birnin New na kasar Amurka, inda yace an sami kaburran ne a wasu kauyuka 2 a yankin Ituri dake da nisan kilo miter 30 da birnin Bunia.
An sami adadin mutane 42 da suka hadar da yara 6 a wani babban kabari a kauyen Nyamamba, haka kuma an ga wasu gawarwaki maza 7 a kauyen Mbogi, a cewar Haq.
Hukumomin yankin sun bayyana cewa kungiyar ‘yan bindiga ta CODECO sun kuma yi awon gaba da wasu mata a hare-haren da aka kai kauyukan.
Ko dai a watan Yulin daya gabata, kungiyar ta CODECO su 7 suka sanar da kawo karshen cin zarafin fararen hula a garin Ituri, musamman Djugu inda suke da karfi. Amma duk da haka suka cigaba da kai hare-hare a yankin.
Akalla mutane 195 ne aka hallaka tun watan disamba a jirin hare-haren da ake zargin kungiyar CODECO da wasu kungiyoyi mas dauke da makamai a cewar MDD. Haka kuma fiye da mutane miliyan 1.5 suka rasa matsugunnin su a lardin Ituri biyo bayan hare-haren.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp